ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi:Yadda Aka Siyasantar Da Cutar Covid-19 Ya Fi Cutar Barna

by CMG Hausa
3 years ago
COVID-19

Kwanan baya, kasar Amurka ta sanar da daukar matakan kayyade shigar baki kasar daga kasar Sin, bisa dalilin da ta bayar na wai “yaduwar cutar a kasar Sin ka iya haifar da sauye-sauyen fasalin cutar”. Amma, ko da gaske ne Amurka ta dauki matakin ne don magance cutar?

A hakika, nau’o’in cutar Covid-19 da yanzu haka ke yaduwa a kasar ta Sin, tuni sun yadu a Amurka da ma sauran wasu kasashen duniya kafin a gano su a kasar Sin. Misali, cutar nau’in BA.5 da ke yaduwa a kasar Sin ta kasance wadda aka fi fuskanta a kasar Amurka a watannin da suka gabata, baya ga cutar nau’in XBB.1.5 da kwanan baya aka gano ta a biranen Shanghai da Hangzhou na gabashin kasar, daidai ta kasance cutar da a halin yanzu taka fi yaduwa a kasar Amurka. A sa’i daya kuma, a yayin da cutar ke yaduwa a fadin duniya, sauye-sauyen fasalin cutar ka iya faruwa ko ina a duniya. Don haka, masana ilmin cututtuka masu yaduwa na kasashe da dama, sun bayyana ra’ayoyinsu na rashin yarda da daukar matakan kayyade shigar baki daga kasar Sin, baya ga kuma wasu hukumomin lafiya da suka hada da cibiyar kandagarkin cututtuka ta Turai suka bayyana cewa, bai dace ba a kayyade shigar baki daga kasar Sin.

Da haka muke ganin cewa, kasar Amurka na daukar matakin ne don siyasantar da cutar.

ADVERTISEMENT

In mun waiwayi shekaru uku da suka wuce, za mu ga cewa, gwamnatin kasar Amurka ba ta taba mai da hankalinta a kan daidaita matsalolin da kasar ke fuskanta ta fannin kadagarkin cutar ba, a maimakon haka ma, tana ta kokarin siyasantar da cutar ne, lamarin da ya sa wannan kasar da ke sahun gaba a duniya ta fannin harkokin kiwon lafiya, ta gamu da munanan hasarorin da bai kamata ba, inda ‘yan kasar sama da miliyan 100 suka harbu da cutar, a yayin da sama da mutanen kasar miliyan 1.08 cutar ta halaka, baya ga kuma yara dubu 250 da suka zama marayu a sakamakon cutar.

Sabanin matakin da Amurka din ta dauka, hukumomin yawon shakatawa, da ofisoshin jakadanci na kasashe da dama da ke kasar Sin a kwanan baya, sun yi maraba da bakin kasar Sin zuwa kasashen su, don fatan ganin babbar kasuwar kasar ta taimaka ga farfado da tattalin arzikinsu, suna kuma fatan hada karfi da karfe tsakanin kasa da kasa, zai fitar da duniya daga mawuyacin halin da ake ciki. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

 

COVID-19
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Matsalar Bazuwar Fyade Zuwa Kan Kananan Yara Maza

Matsalar Bazuwar Fyade Zuwa Kan Kananan Yara Maza

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.