• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shari’ar Zaɓe: Gwamnan Sokoto Ya Kori Sakatarorin Ilimi Na Jihar

by Sulaiman
2 years ago
Gwamnan Sokoto

Gwamna Ahmad Aliyu na jihar Sokoto ya tsige sakatarorin ilimi na kananan hukumomi 23 da ke jiharsa, inda ya umurce su da su mika al’amuran ofisoshinsu ga babban jami’i a kananan hukumominsu.

Wata sanarwa da kakakin gwamnan jihar Abubakar Bawa ya fitar a daren Laraba, ta ce, an tsige sakatarorin ilimin nan take.

  • Yadda Matar Shugaban DSS Ta Yi Barazanar Hana Ni Zama Gwamnan Kano –Abba Gida-Gida

Hakan ya biyo bayan zaman da aka yi a ranar Laraba a kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Sokoto, wadda ta bukaci shugaban makarantar Town Model Primary School da ke Sabon Birni da ke karkashin karamar hukumar Sabon Birni, Ibrahim Abdullahi, ya ba da shaida kan karar da dan takarar gwamna a jam’iyyar PDP, Sa’idu Umar ya gabatar a gaban kotun yana kalubalantar cancantar mataimakin  gwamnan jihar, Ahmad Aliyu na tsayawa takarar gwamna a zaben 2023.

Umar a cikin karar da ya gabatar, ya na kalubalantar cancantar abokin takarar gwamna a jam’iyyar APC, Mohammed Idris Gobir, kan cewa bai halarci makarantar firamare ba.

Sbugaban makarantar ya samu rakiyar Lauyan Sa’idu Umar, S.I. Ameh SAN, zuwa zaman sauraron karar don bayarda shaida tare da gabatar da takardar shaidar shiga makarantar a 1981 da na kammala karatu a shekarar 1987, don tabbatar da cewa Gobir bai halarci makarantar ba kamar yadda ya yi ikirari.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Shugaban zaman sauraron kararrakin zaben, Mai shari’a Haruna Mshelia, ya amince da kwafin takardun da aka gabatar masa yayin da babban lauyan wadanda ake kara, Cif Jecob Ochidi, ya ki amincewa da takardun.

Korar da Ahmad Aliyu ya yi wa sakatarorin ilimi na kananan hukumomin jim kadan bayan kammala zaman kotun, ana kallon hukuncin a matsayin ramuwar gayya da riga-kafi ga irin wannan sheda a kotun zabe, domin shi ma Gwamnan yana fuskantar irin wannan kara ta rashin halartar makaranta a kotun.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Next Post
Li Qiang: Alakar Kasashen Sin Da Faransa Tana Da Ma’ana A Duniya.

Li Qiang: Alakar Kasashen Sin Da Faransa Tana Da Ma'ana A Duniya.

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.