• English
  • Business News
Monday, July 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharudda 17 Da Kungiyar Kwadago Ta Gindaya Wa Gwamnati Kafin Janye Zanga-zanga

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
NLC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) ta ginda sharudda 17 da take neman Shugaban kasa, Bola Tinubu ya cika kafin ta amince ta janye zanga-zangan da ta fara gudanarwa a kasa baki daya.

Kugiyar NLC ta janye zanga-zangar kwanaki biyu da ta shirya bayan kwana daya da farawa. Ta ce ta amince da janye zanga-zangar ne domin tattaunawa da gwamnati ta yi.

  • Kasar Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Taimakawa Jarin Waje
  • Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutane 5, 10 Sun Jikkata A Hanyar Legas Zuwa Ibadan

Shugaban kungiyar kwadagon, Joe Ajaero da mukaddashin babbann sakataren kungiyar, Ismail Bello sun bayyana cewa, “Mun samu nasarar tattaunawa da gwamnati bayan gudanar da zanga-zanga a ranar farko, inda gwamnati ta yi alkawarin cewa za ta yi kokarin kare mutane da kuma ma’aikatan Nijeriya daga wannan tsadar rayuwa da ake ciki.”

A ranar farko na zanga-zangar, kungiyar kwadago ta kai ka wa shugaban kasa wasika mai taken, “Kawo karshen matsaloli da ke faru a kasar nan tun da wuri.”

Wasikar da ke dauke da sa hannun shugaban kwadago, Joe Ajaero ta yi kira ga majalisar zartarwa ta kasa da ta duba bukatun kungiyar kwadago a daidai lokacin da ‘yan kasa da ma’aikata ke fama da yunwa da kuma fatara.

Labarai Masu Nasaba

‘Ka Da Ki Kuskura Ki Zo Majalisar Tarayya’, Majalisar Dattawa Ta Sake Yi Wa Natasha Gargaɗi

Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

Sharuddan da kungiyar kwadagon ta gindaya sun hada da samar da wani shiri na gaggawa da zai magance matsalolin da kasar nan take fuskanta a halin yanzu, wanda ta bukaci daukan matakai da za su dakile tsadar rayuwa a kasar na da kuma samun wadataccen abinci.

“Muna bayar da shawarar a sake bude dukkan iyakokin kasar nann domin samun damar shigo da abinci, siminti da kuma sauran kayayyakin bukatu. A dauki matakan kan gaggawa da za su tabbatar da samar da abinci a kasa, ciki har da tabbatar da tsare gonaki ta yadda manoma za su ci gaba da gudanar da harkokin noma.

“Muna so a dage biyan haraji ga kananan ‘yan kasuwa da ke fadin kasar nan. Cika alkawarin da aka yi mana tun a ranar 2 ga Oktoban 2023, yarjejeniyar da muka cimma tsakaninmu da gwamnati.

“Sayan matocin bas masu amfani da lantarki a dukkan jihohin kasar nan, domin sukaka harkokin sufuri da rage dogaro da man fetur.
“Dakatar da karin kudin makaranta a daukacin fadin kasar nan. Rage haraji ga masu shigo da kayayyaki da magugguna da zai rage wahalhalun da marasa lafiya ke ciki.

“Bai wa dukkan gwamnatoci umurnin biyan mafi karancin albashi da alawus-alawus na mataikata da kuma biyan kudin fansho. Biyan kudaden rage radadi ga mabukatan da aka yi wa rajista nan take. Rage harajin ma’aikata da ke daukan naira 100,000 a duk wata da kuma wadanda suke daukan kasa da naira 500,000 a duk wata.

“Cire haraji kan kayayyakin da ake amfani da su kai tsaye. Bayar da umurnin saya da amfani da kayayyakin da ake sarrafawa a Nijeriya da zai iya bunkasa kayayyakin da samar da ayyukan yi ga ‘yan kasa. Rage kashe kudaden gwamnati a dukkan mataki na kasar nan. Watsi da dukkan manufofin asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) da kuma bankin duniya a Nijeriya, domin ba sa yin aiki a Nijeriya sai dai suna kara mana matsin rayuwa. Gaggawan aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma kan biyan mafi karancin albashi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kayyade Tsadar AureNlcZanga-zangar adawa da yunwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Gwamnati Ke Kara Shan Matsin Lamba A Kan Yunwa

Next Post

Sheikh Daurawa Ya Sauka Daga Muƙaminsa Na Shugaban Hisbah Kano

Related

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Ka Da Ki Kuskura Ki Zo Majalisar Tarayya’, Majalisar Dattawa Ta Sake Yi Wa Natasha Gargaɗi

8 hours ago
Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC
Labarai

Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

9 hours ago
Mutane 2 Sun Gurfana Gaban Alƙali Kan Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
Labarai

Mutane 2 Sun Gurfana Gaban Alƙali Kan Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

14 hours ago
Bayan Shekaru 7 Yana Ɓoye, NDLEA Ta Cafke Babban Dillalin Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Bayan Shekaru 7 Yana Ɓoye, NDLEA Ta Cafke Babban Dillalin Ƙwayoyi

15 hours ago
Yanzu Haka Muna Bincikar Gwamnoni 18 – Shugaban EFCC
Labarai

Yanzu Haka Muna Bincikar Gwamnoni 18 – Shugaban EFCC

16 hours ago
Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Zama Sakatariyar Kungiyar Yaƙi Da Cutar Daji
Labarai

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Zama Sakatariyar Kungiyar Yaƙi Da Cutar Daji

17 hours ago
Next Post
Kotu Ta Aike Da Ramlat Princess Zuwa Gidan Gyaran Hali Na Kano Tsawon Watanni Bakwai

Sheikh Daurawa Ya Sauka Daga Muƙaminsa Na Shugaban Hisbah Kano

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Kera Kayan Likitanci Na Duniya: Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Babban Ginshiki Ne

Kamfanonin Kera Kayan Likitanci Na Duniya: Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Babban Ginshiki Ne

July 20, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

‘Ka Da Ki Kuskura Ki Zo Majalisar Tarayya’, Majalisar Dattawa Ta Sake Yi Wa Natasha Gargaɗi

July 20, 2025
An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

July 20, 2025
Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

July 20, 2025
Jimillar Sayar Da Kayayyakin Masarufi Ta Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Triliyan 50 A Bana

Jimillar Sayar Da Kayayyakin Masarufi Ta Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Triliyan 50 A Bana

July 20, 2025
Mataimakin Shugaban Kamfanin Panasonic: Kamfanonin Sin Dake Samar Da Sassan Kayayyaki Ga Kamfaninsa Sun Kai Dubu 6

Mataimakin Shugaban Kamfanin Panasonic: Kamfanonin Sin Dake Samar Da Sassan Kayayyaki Ga Kamfaninsa Sun Kai Dubu 6

July 20, 2025
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Aiwatar Da Manyan Ayyukan Kasa Cikin Inganci

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Aiwatar Da Manyan Ayyukan Kasa Cikin Inganci

July 20, 2025
Mutane 2 Sun Gurfana Gaban Alƙali Kan Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

Mutane 2 Sun Gurfana Gaban Alƙali Kan Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

July 20, 2025
Bayan Shekaru 7 Yana Ɓoye, NDLEA Ta Cafke Babban Dillalin Ƙwayoyi

Bayan Shekaru 7 Yana Ɓoye, NDLEA Ta Cafke Babban Dillalin Ƙwayoyi

July 20, 2025
Yanzu Haka Muna Bincikar Gwamnoni 18 – Shugaban EFCC

Yanzu Haka Muna Bincikar Gwamnoni 18 – Shugaban EFCC

July 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.