• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharudda 17 Da Kungiyar Kwadago Ta Gindaya Wa Gwamnati Kafin Janye Zanga-zanga

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
NLC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) ta ginda sharudda 17 da take neman Shugaban kasa, Bola Tinubu ya cika kafin ta amince ta janye zanga-zangan da ta fara gudanarwa a kasa baki daya.

Kugiyar NLC ta janye zanga-zangar kwanaki biyu da ta shirya bayan kwana daya da farawa. Ta ce ta amince da janye zanga-zangar ne domin tattaunawa da gwamnati ta yi.

  • Kasar Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Taimakawa Jarin Waje
  • Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutane 5, 10 Sun Jikkata A Hanyar Legas Zuwa Ibadan

Shugaban kungiyar kwadagon, Joe Ajaero da mukaddashin babbann sakataren kungiyar, Ismail Bello sun bayyana cewa, “Mun samu nasarar tattaunawa da gwamnati bayan gudanar da zanga-zanga a ranar farko, inda gwamnati ta yi alkawarin cewa za ta yi kokarin kare mutane da kuma ma’aikatan Nijeriya daga wannan tsadar rayuwa da ake ciki.”

A ranar farko na zanga-zangar, kungiyar kwadago ta kai ka wa shugaban kasa wasika mai taken, “Kawo karshen matsaloli da ke faru a kasar nan tun da wuri.”

Wasikar da ke dauke da sa hannun shugaban kwadago, Joe Ajaero ta yi kira ga majalisar zartarwa ta kasa da ta duba bukatun kungiyar kwadago a daidai lokacin da ‘yan kasa da ma’aikata ke fama da yunwa da kuma fatara.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Sharuddan da kungiyar kwadagon ta gindaya sun hada da samar da wani shiri na gaggawa da zai magance matsalolin da kasar nan take fuskanta a halin yanzu, wanda ta bukaci daukan matakai da za su dakile tsadar rayuwa a kasar na da kuma samun wadataccen abinci.

“Muna bayar da shawarar a sake bude dukkan iyakokin kasar nann domin samun damar shigo da abinci, siminti da kuma sauran kayayyakin bukatu. A dauki matakan kan gaggawa da za su tabbatar da samar da abinci a kasa, ciki har da tabbatar da tsare gonaki ta yadda manoma za su ci gaba da gudanar da harkokin noma.

“Muna so a dage biyan haraji ga kananan ‘yan kasuwa da ke fadin kasar nan. Cika alkawarin da aka yi mana tun a ranar 2 ga Oktoban 2023, yarjejeniyar da muka cimma tsakaninmu da gwamnati.

“Sayan matocin bas masu amfani da lantarki a dukkan jihohin kasar nan, domin sukaka harkokin sufuri da rage dogaro da man fetur.
“Dakatar da karin kudin makaranta a daukacin fadin kasar nan. Rage haraji ga masu shigo da kayayyaki da magugguna da zai rage wahalhalun da marasa lafiya ke ciki.

“Bai wa dukkan gwamnatoci umurnin biyan mafi karancin albashi da alawus-alawus na mataikata da kuma biyan kudin fansho. Biyan kudaden rage radadi ga mabukatan da aka yi wa rajista nan take. Rage harajin ma’aikata da ke daukan naira 100,000 a duk wata da kuma wadanda suke daukan kasa da naira 500,000 a duk wata.

“Cire haraji kan kayayyakin da ake amfani da su kai tsaye. Bayar da umurnin saya da amfani da kayayyakin da ake sarrafawa a Nijeriya da zai iya bunkasa kayayyakin da samar da ayyukan yi ga ‘yan kasa. Rage kashe kudaden gwamnati a dukkan mataki na kasar nan. Watsi da dukkan manufofin asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) da kuma bankin duniya a Nijeriya, domin ba sa yin aiki a Nijeriya sai dai suna kara mana matsin rayuwa. Gaggawan aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma kan biyan mafi karancin albashi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kayyade Tsadar AureNlcZanga-zangar adawa da yunwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Gwamnati Ke Kara Shan Matsin Lamba A Kan Yunwa

Next Post

Sheikh Daurawa Ya Sauka Daga Muƙaminsa Na Shugaban Hisbah Kano

Related

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

10 hours ago
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam
Labarai

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

11 hours ago
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
Tsaro

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

14 hours ago
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
Manyan Labarai

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

15 hours ago
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

16 hours ago
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
Manyan Labarai

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

17 hours ago
Next Post
Kotu Ta Aike Da Ramlat Princess Zuwa Gidan Gyaran Hali Na Kano Tsawon Watanni Bakwai

Sheikh Daurawa Ya Sauka Daga Muƙaminsa Na Shugaban Hisbah Kano

LABARAI MASU NASABA

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

August 11, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

Sin Ta Gudanar Da Gwajin Farko Na Gagarumin Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Dakarun Japan

August 11, 2025
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

August 10, 2025
Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu

Sin Na Gaggauta Gina Tsarin Tattalin Arziki Mai Kiyaye Muhallin Halittu

August 11, 2025
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.