ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharudda 17 Da Kungiyar Kwadago Ta Gindaya Wa Gwamnati Kafin Janye Zanga-zanga

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
NLC

Kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) ta ginda sharudda 17 da take neman Shugaban kasa, Bola Tinubu ya cika kafin ta amince ta janye zanga-zangan da ta fara gudanarwa a kasa baki daya.

Kugiyar NLC ta janye zanga-zangar kwanaki biyu da ta shirya bayan kwana daya da farawa. Ta ce ta amince da janye zanga-zangar ne domin tattaunawa da gwamnati ta yi.

  • Kasar Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Taimakawa Jarin Waje
  • Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutane 5, 10 Sun Jikkata A Hanyar Legas Zuwa Ibadan

Shugaban kungiyar kwadagon, Joe Ajaero da mukaddashin babbann sakataren kungiyar, Ismail Bello sun bayyana cewa, “Mun samu nasarar tattaunawa da gwamnati bayan gudanar da zanga-zanga a ranar farko, inda gwamnati ta yi alkawarin cewa za ta yi kokarin kare mutane da kuma ma’aikatan Nijeriya daga wannan tsadar rayuwa da ake ciki.”

ADVERTISEMENT

A ranar farko na zanga-zangar, kungiyar kwadago ta kai ka wa shugaban kasa wasika mai taken, “Kawo karshen matsaloli da ke faru a kasar nan tun da wuri.”

Wasikar da ke dauke da sa hannun shugaban kwadago, Joe Ajaero ta yi kira ga majalisar zartarwa ta kasa da ta duba bukatun kungiyar kwadago a daidai lokacin da ‘yan kasa da ma’aikata ke fama da yunwa da kuma fatara.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sharuddan da kungiyar kwadagon ta gindaya sun hada da samar da wani shiri na gaggawa da zai magance matsalolin da kasar nan take fuskanta a halin yanzu, wanda ta bukaci daukan matakai da za su dakile tsadar rayuwa a kasar na da kuma samun wadataccen abinci.

“Muna bayar da shawarar a sake bude dukkan iyakokin kasar nann domin samun damar shigo da abinci, siminti da kuma sauran kayayyakin bukatu. A dauki matakan kan gaggawa da za su tabbatar da samar da abinci a kasa, ciki har da tabbatar da tsare gonaki ta yadda manoma za su ci gaba da gudanar da harkokin noma.

“Muna so a dage biyan haraji ga kananan ‘yan kasuwa da ke fadin kasar nan. Cika alkawarin da aka yi mana tun a ranar 2 ga Oktoban 2023, yarjejeniyar da muka cimma tsakaninmu da gwamnati.

“Sayan matocin bas masu amfani da lantarki a dukkan jihohin kasar nan, domin sukaka harkokin sufuri da rage dogaro da man fetur.
“Dakatar da karin kudin makaranta a daukacin fadin kasar nan. Rage haraji ga masu shigo da kayayyaki da magugguna da zai rage wahalhalun da marasa lafiya ke ciki.

“Bai wa dukkan gwamnatoci umurnin biyan mafi karancin albashi da alawus-alawus na mataikata da kuma biyan kudin fansho. Biyan kudaden rage radadi ga mabukatan da aka yi wa rajista nan take. Rage harajin ma’aikata da ke daukan naira 100,000 a duk wata da kuma wadanda suke daukan kasa da naira 500,000 a duk wata.

“Cire haraji kan kayayyakin da ake amfani da su kai tsaye. Bayar da umurnin saya da amfani da kayayyakin da ake sarrafawa a Nijeriya da zai iya bunkasa kayayyakin da samar da ayyukan yi ga ‘yan kasa. Rage kashe kudaden gwamnati a dukkan mataki na kasar nan. Watsi da dukkan manufofin asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) da kuma bankin duniya a Nijeriya, domin ba sa yin aiki a Nijeriya sai dai suna kara mana matsin rayuwa. Gaggawan aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma kan biyan mafi karancin albashi.”

Kwadago
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Kotu Ta Aike Da Ramlat Princess Zuwa Gidan Gyaran Hali Na Kano Tsawon Watanni Bakwai

Sheikh Daurawa Ya Sauka Daga Muƙaminsa Na Shugaban Hisbah Kano

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.