ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, September 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharudda 17 Da Kungiyar Kwadago Ta Gindaya Wa Gwamnati Kafin Janye Zanga-zanga

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
NLC

Kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) ta ginda sharudda 17 da take neman Shugaban kasa, Bola Tinubu ya cika kafin ta amince ta janye zanga-zangan da ta fara gudanarwa a kasa baki daya.

Kugiyar NLC ta janye zanga-zangar kwanaki biyu da ta shirya bayan kwana daya da farawa. Ta ce ta amince da janye zanga-zangar ne domin tattaunawa da gwamnati ta yi.

  • Kasar Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Taimakawa Jarin Waje
  • Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutane 5, 10 Sun Jikkata A Hanyar Legas Zuwa Ibadan

Shugaban kungiyar kwadagon, Joe Ajaero da mukaddashin babbann sakataren kungiyar, Ismail Bello sun bayyana cewa, “Mun samu nasarar tattaunawa da gwamnati bayan gudanar da zanga-zanga a ranar farko, inda gwamnati ta yi alkawarin cewa za ta yi kokarin kare mutane da kuma ma’aikatan Nijeriya daga wannan tsadar rayuwa da ake ciki.”

ADVERTISEMENT

A ranar farko na zanga-zangar, kungiyar kwadago ta kai ka wa shugaban kasa wasika mai taken, “Kawo karshen matsaloli da ke faru a kasar nan tun da wuri.”

Wasikar da ke dauke da sa hannun shugaban kwadago, Joe Ajaero ta yi kira ga majalisar zartarwa ta kasa da ta duba bukatun kungiyar kwadago a daidai lokacin da ‘yan kasa da ma’aikata ke fama da yunwa da kuma fatara.

LABARAI MASU NASABA

Na Miƙa Kaina Ga Hukumomin Tsaro – Sanata Shehu Buba

Babu Dalilin Da Zai Sa Nijeriya Yin Talauci – Obasanjo

Sharuddan da kungiyar kwadagon ta gindaya sun hada da samar da wani shiri na gaggawa da zai magance matsalolin da kasar nan take fuskanta a halin yanzu, wanda ta bukaci daukan matakai da za su dakile tsadar rayuwa a kasar na da kuma samun wadataccen abinci.

“Muna bayar da shawarar a sake bude dukkan iyakokin kasar nann domin samun damar shigo da abinci, siminti da kuma sauran kayayyakin bukatu. A dauki matakan kan gaggawa da za su tabbatar da samar da abinci a kasa, ciki har da tabbatar da tsare gonaki ta yadda manoma za su ci gaba da gudanar da harkokin noma.

“Muna so a dage biyan haraji ga kananan ‘yan kasuwa da ke fadin kasar nan. Cika alkawarin da aka yi mana tun a ranar 2 ga Oktoban 2023, yarjejeniyar da muka cimma tsakaninmu da gwamnati.

“Sayan matocin bas masu amfani da lantarki a dukkan jihohin kasar nan, domin sukaka harkokin sufuri da rage dogaro da man fetur.
“Dakatar da karin kudin makaranta a daukacin fadin kasar nan. Rage haraji ga masu shigo da kayayyaki da magugguna da zai rage wahalhalun da marasa lafiya ke ciki.

“Bai wa dukkan gwamnatoci umurnin biyan mafi karancin albashi da alawus-alawus na mataikata da kuma biyan kudin fansho. Biyan kudaden rage radadi ga mabukatan da aka yi wa rajista nan take. Rage harajin ma’aikata da ke daukan naira 100,000 a duk wata da kuma wadanda suke daukan kasa da naira 500,000 a duk wata.

“Cire haraji kan kayayyakin da ake amfani da su kai tsaye. Bayar da umurnin saya da amfani da kayayyakin da ake sarrafawa a Nijeriya da zai iya bunkasa kayayyakin da samar da ayyukan yi ga ‘yan kasa. Rage kashe kudaden gwamnati a dukkan mataki na kasar nan. Watsi da dukkan manufofin asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) da kuma bankin duniya a Nijeriya, domin ba sa yin aiki a Nijeriya sai dai suna kara mana matsin rayuwa. Gaggawan aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma kan biyan mafi karancin albashi.”

Kwadago
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Jam’iyyar APC Ce Za Ta Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Da Gwamnoni A Nijeriya -Dikko Raɗɗa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

MASU ALAKA

Na Miƙa Kaina Ga Hukumomin Tsaro – Sanata Shehu Buba
Labarai

Na Miƙa Kaina Ga Hukumomin Tsaro – Sanata Shehu Buba

September 14, 2026
Kwadago
Labarai

Babu Dalilin Da Zai Sa Nijeriya Yin Talauci – Obasanjo

September 14, 2026
Kwadago
Labarai

Air Peace Da United Nigeria, Jirage 2 Masu Latti Sosai Watan Agusta — NCAA

September 14, 2026
Next Post
Kotu Ta Aike Da Ramlat Princess Zuwa Gidan Gyaran Hali Na Kano Tsawon Watanni Bakwai

Sheikh Daurawa Ya Sauka Daga Muƙaminsa Na Shugaban Hisbah Kano

LABARAI MASU NASABA

Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

September 14, 2026
Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

September 14, 2026
Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

September 14, 2026
Hadin Gwiwar BRICS Na Jagorantar Hadin Kan Kasashe Masu Tasowa Da Dogaro Da Karfin Kansu

Hadin Gwiwar BRICS Na Jagorantar Hadin Kan Kasashe Masu Tasowa Da Dogaro Da Karfin Kansu

September 14, 2026
Na Miƙa Kaina Ga Hukumomin Tsaro – Sanata Shehu Buba

Na Miƙa Kaina Ga Hukumomin Tsaro – Sanata Shehu Buba

September 14, 2026
Sin Na Shirin Fadada Samar Da Hidimomin Reno Da Na Kiwon Lafiyar Yara Masu Rahusa

Sin Na Shirin Fadada Samar Da Hidimomin Reno Da Na Kiwon Lafiyar Yara Masu Rahusa

September 14, 2026
Kwadago

Babu Dalilin Da Zai Sa Nijeriya Yin Talauci – Obasanjo

September 14, 2026
Gudummawar Da Hada-Hadar Ba Da Hidima Ta Sin Take Kawo Wa Duniya

Gudummawar Da Hada-Hadar Ba Da Hidima Ta Sin Take Kawo Wa Duniya

September 14, 2026
Kwadago

Air Peace Da United Nigeria, Jirage 2 Masu Latti Sosai Watan Agusta — NCAA

September 14, 2026
Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka

September 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.