• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar BRI Ta Kawo Manyan Sauye-sauye A Duniya Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

by CGTN Hausa
2 years ago
BRI

Za a gudanar da taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar kasa da kasa kan raya shawarar “ziri daya da hanya daya”, wato BRF a takaice karo na 3 daga ranar 17 zuwa ranar 18 ga watan Oktoba. Alkaluman da Sin ta fitar a hukumance na nuna cewa, dandalin tattautawar na wannan karo ya jawo hankulan wakilan da suka fito daga kasashe fiye da 140 da kuma kungiyoyin duniya fiye da 30, su halarci taron don inganta ci gaba tare. Dalilin da ya sa dandalin tattaunawar ya shahara a duniya, a cikin shekaru 10 da suka gabata, aikin hadin gwiwar shawarar “ziri daya da hanya daya”, ya kawo sabbin sauye-sauye a duniya.

A cikin shekaru 10 da suka gabata, an gudanar da ayyukan hadin gwiwa fiye da 3000 don gina shawarar “ziri daya da hanya daya”, wato BRI a takaice, wadanda suka kai ga zuba jarin triliyoyin dalar Amurka. Ya zuwa karshen watan Yunin wannan shekara, Sin ta sanya hannu kan takardun hadin gwiwa fiye da 200 kan shirin raya shawarar “ziri daya da hanya daya” tare da kasashe fiye da 150 da kuma kungiyoyi fiye da 30.

  • Sin Ta Kai Daukin Gaggawa Ga Falasdinawa
  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Zai Halarci Bikin Bude Taron BRF

Binciken bankin duniya ya nuna cewa, gudanar da shawarar “ziri daya da hanya daya” yadda ya kamata, zai kara habaka cinikayya tsakanin kasashen da suka amince da shawarar zuwa 4.1%, kana nan shekarar 2030, ana sa ran, shawarar za ta samarwa duniya kudaden shiga har dalar Amurka tiriliyan 1.6 a duk shekara. Kuma ana sa ran za ta cire mutane miliyan 7.6 daga kasashe masu hadin gwiwa daga matsanancin talauci.

Abubuwan da shawarar “ziri daya da hanya daya” ta kawo ba moriyar tattalin arziki kawai ba ne, har ma da sabon tsarin mulki. Sin ta zuba jari don kafa asusun hanyar siliki, tare da kafa bankin zuba jari na kayayyakin more rayuwa na Asiya tare da kasashen da abin ya shafa, wanda ya fadada hanyoyin zuba jari da samar da kudade don gina kasashe tare da inganta tsarin tafiyar da harkokin tattalin arzikin duniya. Manufar shawarar “ziri daya da hanya daya” ita ce zamanintar da juna tare, tare da taimakawa wajen kara karfin kasashe na raya kansu. Daga raba kwarewar ci gaba zuwa horar da kwararru tare, daga bunkasa cinikayyar yanar gizo tsakanin kasa da kasa zuwa tattauna shirin ci gaba, Sin ta kawo sabbin damammaki ga duniya, tare da habaka hanyar zuwa zamanintarwa ta bil’adama.

Duk da cewa, shawarar “ziri daya da hanya daya” ta samo asali ne daga kasar Sin, amma shawara ce ta duniya baki daya, kuma ta kawo alheri ga dukkanin bil’adama. Kamar yadda kakakin majalisar al’ummar Serbia Vladimir Orlić ya ce, shawarar “ziri daya da hanya daya” hanya ce ta nan gaba. (Safiyah Ma)

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi
Daga Birnin Sin

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori
Daga Birnin Sin

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan
Daga Birnin Sin

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Next Post
Kasashen Yamma Suna Tsotse Jinin ‘Yan Afirka Yayin Da Kasar Sin Ke Kawo Bege

Kasashen Yamma Suna Tsotse Jinin 'Yan Afirka Yayin Da Kasar Sin Ke Kawo Bege

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.