• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar BRI Ta Kawo Manyan Sauye-sauye A Duniya Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shawarar BRI Ta Kawo Manyan Sauye-sauye A Duniya Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Za a gudanar da taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar kasa da kasa kan raya shawarar “ziri daya da hanya daya”, wato BRF a takaice karo na 3 daga ranar 17 zuwa ranar 18 ga watan Oktoba. Alkaluman da Sin ta fitar a hukumance na nuna cewa, dandalin tattautawar na wannan karo ya jawo hankulan wakilan da suka fito daga kasashe fiye da 140 da kuma kungiyoyin duniya fiye da 30, su halarci taron don inganta ci gaba tare. Dalilin da ya sa dandalin tattaunawar ya shahara a duniya, a cikin shekaru 10 da suka gabata, aikin hadin gwiwar shawarar “ziri daya da hanya daya”, ya kawo sabbin sauye-sauye a duniya.

A cikin shekaru 10 da suka gabata, an gudanar da ayyukan hadin gwiwa fiye da 3000 don gina shawarar “ziri daya da hanya daya”, wato BRI a takaice, wadanda suka kai ga zuba jarin triliyoyin dalar Amurka. Ya zuwa karshen watan Yunin wannan shekara, Sin ta sanya hannu kan takardun hadin gwiwa fiye da 200 kan shirin raya shawarar “ziri daya da hanya daya” tare da kasashe fiye da 150 da kuma kungiyoyi fiye da 30.

  • Sin Ta Kai Daukin Gaggawa Ga Falasdinawa
  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Zai Halarci Bikin Bude Taron BRF

Binciken bankin duniya ya nuna cewa, gudanar da shawarar “ziri daya da hanya daya” yadda ya kamata, zai kara habaka cinikayya tsakanin kasashen da suka amince da shawarar zuwa 4.1%, kana nan shekarar 2030, ana sa ran, shawarar za ta samarwa duniya kudaden shiga har dalar Amurka tiriliyan 1.6 a duk shekara. Kuma ana sa ran za ta cire mutane miliyan 7.6 daga kasashe masu hadin gwiwa daga matsanancin talauci.

Abubuwan da shawarar “ziri daya da hanya daya” ta kawo ba moriyar tattalin arziki kawai ba ne, har ma da sabon tsarin mulki. Sin ta zuba jari don kafa asusun hanyar siliki, tare da kafa bankin zuba jari na kayayyakin more rayuwa na Asiya tare da kasashen da abin ya shafa, wanda ya fadada hanyoyin zuba jari da samar da kudade don gina kasashe tare da inganta tsarin tafiyar da harkokin tattalin arzikin duniya. Manufar shawarar “ziri daya da hanya daya” ita ce zamanintar da juna tare, tare da taimakawa wajen kara karfin kasashe na raya kansu. Daga raba kwarewar ci gaba zuwa horar da kwararru tare, daga bunkasa cinikayyar yanar gizo tsakanin kasa da kasa zuwa tattauna shirin ci gaba, Sin ta kawo sabbin damammaki ga duniya, tare da habaka hanyar zuwa zamanintarwa ta bil’adama.

Duk da cewa, shawarar “ziri daya da hanya daya” ta samo asali ne daga kasar Sin, amma shawara ce ta duniya baki daya, kuma ta kawo alheri ga dukkanin bil’adama. Kamar yadda kakakin majalisar al’ummar Serbia Vladimir Orlić ya ce, shawarar “ziri daya da hanya daya” hanya ce ta nan gaba. (Safiyah Ma)

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: RashaShawarar ziri dayaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganawa Da Xi Jinping: Ina Godiya Gare Shi Bisa Cimma Burina

Next Post

Kasashen Yamma Suna Tsotse Jinin ‘Yan Afirka Yayin Da Kasar Sin Ke Kawo Bege

Related

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

1 hour ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

2 hours ago
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

14 hours ago
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

18 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

19 hours ago
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

20 hours ago
Next Post
Kasashen Yamma Suna Tsotse Jinin ‘Yan Afirka Yayin Da Kasar Sin Ke Kawo Bege

Kasashen Yamma Suna Tsotse Jinin 'Yan Afirka Yayin Da Kasar Sin Ke Kawo Bege

LABARAI MASU NASABA

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.