• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Rukunin Al’umma

by CGTN Hausa
2 years ago
Ziri daya

Baya ga kasashe da yankuna da kungiyoyin kasa da kasa da suka amince da shawarar “ziri daya da hanya daya”, a gabar da hankalin duniya ya koma ga taron kolin hadin gwiwar shawarar dake gudana a birnin Beijing na kasar Sin, wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a da cibiyar nazarin watsa labaran kasa da kasa a sabon zamani ta tattara, karkashin jagorancin kafar talabijin ta CGTN, dake karkashin rukunin kafofin watsa labarai na kasar Sin CMG, da jami’ar Renmin ta kasar Sin, albarkacin cikar shawarar da kasar Sin ta gabatar shekaru goma cif da kafuwa, matasa dake tsakanin shekaru 18 zuwa 44, wadanda suka bayyana ra’ayinsu, sun amince da tunanin shawarar, da sakamakon da aka samu, tun bayan kafa shawarar shekaru goma da suka gabata zuwa yanzu.

Yayin kada kuri’ar jin ra’ayin jama’ar, an lura cewa, kaso 84.6 cikin 100 na matasan da suka bayyana ra’ayinsu, sun amince da “ruhin hanyar siliki” da kasar Sin ta gabatar, wato “hadin gwiwa cikin lumana, da bude kofa tare da yin hakuri, da koyi da juna, da cin moriyar juna domin samun ci gaba tare” . Bugu da kari, kuri’ar jin ra’ayin jama’ar ta nuna cewa, matasa masu karancin shekaru sun fi amincewa da shawarar, yayin da kaso 88.8 cikin 100 na matasa masu shekaru 18 zuwa 24, suka amince da “ruhin hanyar siliki”.

  • IMF Ta Yi Hasashen Tattalin Arzikin Kasar Sin Zai Karu Da Kaso 5 A Bana
  • Kasashe Masu Tasowa Da Abokai Sun Goyi Bayan Matsayin Kasar Sin Mai Adalci A Taron MDD

An gudanar da kuri’ar jin ra’ayin jama’ar ce ga matasa 3,857 dake kasashe 35, a kasashen Amurka, da Birtaniya, da Japan, da Afirka ta kudu, da Argentina, da Thailand, da Najeriya, da Peru, da Mexico da sauransu.  Baya ga rukunin matasa, shi ma shugaban kasar Sri Lanka Ranil Wickremesinghe ya yi nuni da cewa, tun daga farkon taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar kasa da kasa kan shawarar “ziri daya da hanya daya” karo na farko a shekarar 2017 zuwa dandalin tattaunawar na biyu, sannan kuma ya zuwa yau, yanayin duniya ya canja. Musamman, yadda cutar COVID-19 ta yi mummunan tasiri ga tattalin arzikin kowace kasa.

A yayin da duniya ke fama da sabbin matsaloli da manyan kalubaloli, yana fatan samun mafita ta hanyar shiga cikin hadin gwiwar kasa da kasa kan shawarar “ziri daya da hanya daya”. Manufar shawarar “ziri daya da hanya daya” ita ce zamanintar da juna tare, da taimakawa wajen kara karfin kasashe na raya kansu. Daga raba kwarewar ci gaba zuwa horar da kwararru tare, daga bunkasa cinikayyar yanar gizo tsakanin kasa da kasa zuwa tattauna shirin ci gaba, Sin ta kawo sabbin damammaki ga duniya, tare da habaka hanyar zuwa zamanintarwa ta bil’adama. A jawabin da shugaba Xi Jinping ya gabatar yayin bude taron hadin gwiwar shawawar karo na uku, ya bayyana cewa, ya dace mu hada kai wajen fuskantar kalubalolin dake gabanmu, ta yadda za a samar da wata makoma mai haske ga ’ya’yanmu da jikokinmu

Duk da cewa, shawarar “ziri daya da hanya daya” ta samo asali ne daga kasar Sin, amma shawarar ce ta duniya baki daya, kuma ta kawo alheri ga dukkanin bil’adama. (Ibrahim Yaya)

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika
Daga Birnin Sin

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Next Post
Tabbatar Da Daidaito Da Cin Moriyar Juna Suna Cikin Babban Ruhin Shawarar BRI

Tabbatar Da Daidaito Da Cin Moriyar Juna Suna Cikin Babban Ruhin Shawarar BRI

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.