ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Rukunin Al’umma

by CGTN Hausa
3 years ago
Ziri daya

Baya ga kasashe da yankuna da kungiyoyin kasa da kasa da suka amince da shawarar “ziri daya da hanya daya”, a gabar da hankalin duniya ya koma ga taron kolin hadin gwiwar shawarar dake gudana a birnin Beijing na kasar Sin, wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a da cibiyar nazarin watsa labaran kasa da kasa a sabon zamani ta tattara, karkashin jagorancin kafar talabijin ta CGTN, dake karkashin rukunin kafofin watsa labarai na kasar Sin CMG, da jami’ar Renmin ta kasar Sin, albarkacin cikar shawarar da kasar Sin ta gabatar shekaru goma cif da kafuwa, matasa dake tsakanin shekaru 18 zuwa 44, wadanda suka bayyana ra’ayinsu, sun amince da tunanin shawarar, da sakamakon da aka samu, tun bayan kafa shawarar shekaru goma da suka gabata zuwa yanzu.

Yayin kada kuri’ar jin ra’ayin jama’ar, an lura cewa, kaso 84.6 cikin 100 na matasan da suka bayyana ra’ayinsu, sun amince da “ruhin hanyar siliki” da kasar Sin ta gabatar, wato “hadin gwiwa cikin lumana, da bude kofa tare da yin hakuri, da koyi da juna, da cin moriyar juna domin samun ci gaba tare” . Bugu da kari, kuri’ar jin ra’ayin jama’ar ta nuna cewa, matasa masu karancin shekaru sun fi amincewa da shawarar, yayin da kaso 88.8 cikin 100 na matasa masu shekaru 18 zuwa 24, suka amince da “ruhin hanyar siliki”.

  • IMF Ta Yi Hasashen Tattalin Arzikin Kasar Sin Zai Karu Da Kaso 5 A Bana
  • Kasashe Masu Tasowa Da Abokai Sun Goyi Bayan Matsayin Kasar Sin Mai Adalci A Taron MDD

An gudanar da kuri’ar jin ra’ayin jama’ar ce ga matasa 3,857 dake kasashe 35, a kasashen Amurka, da Birtaniya, da Japan, da Afirka ta kudu, da Argentina, da Thailand, da Najeriya, da Peru, da Mexico da sauransu.  Baya ga rukunin matasa, shi ma shugaban kasar Sri Lanka Ranil Wickremesinghe ya yi nuni da cewa, tun daga farkon taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar kasa da kasa kan shawarar “ziri daya da hanya daya” karo na farko a shekarar 2017 zuwa dandalin tattaunawar na biyu, sannan kuma ya zuwa yau, yanayin duniya ya canja. Musamman, yadda cutar COVID-19 ta yi mummunan tasiri ga tattalin arzikin kowace kasa.

ADVERTISEMENT

A yayin da duniya ke fama da sabbin matsaloli da manyan kalubaloli, yana fatan samun mafita ta hanyar shiga cikin hadin gwiwar kasa da kasa kan shawarar “ziri daya da hanya daya”. Manufar shawarar “ziri daya da hanya daya” ita ce zamanintar da juna tare, da taimakawa wajen kara karfin kasashe na raya kansu. Daga raba kwarewar ci gaba zuwa horar da kwararru tare, daga bunkasa cinikayyar yanar gizo tsakanin kasa da kasa zuwa tattauna shirin ci gaba, Sin ta kawo sabbin damammaki ga duniya, tare da habaka hanyar zuwa zamanintarwa ta bil’adama. A jawabin da shugaba Xi Jinping ya gabatar yayin bude taron hadin gwiwar shawawar karo na uku, ya bayyana cewa, ya dace mu hada kai wajen fuskantar kalubalolin dake gabanmu, ta yadda za a samar da wata makoma mai haske ga ’ya’yanmu da jikokinmu

Duk da cewa, shawarar “ziri daya da hanya daya” ta samo asali ne daga kasar Sin, amma shawarar ce ta duniya baki daya, kuma ta kawo alheri ga dukkanin bil’adama. (Ibrahim Yaya)

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

 

Ziri daya
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Tabbatar Da Daidaito Da Cin Moriyar Juna Suna Cikin Babban Ruhin Shawarar BRI

Tabbatar Da Daidaito Da Cin Moriyar Juna Suna Cikin Babban Ruhin Shawarar BRI

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.