• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ta Zama Nagge Dadi Goma

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ta Zama Nagge Dadi Goma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kafin fara hadin gwiwa a karkashin shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” a tsakanin Kasar Sin da Afirka, kimanin shekara 10 da suka gabata, galibin mutanen Afirka kan kwana su tashi da burin ganin yaushe za su more rayuwarsu irin yadda ‘yan kasashen da suka ci gaba a duniya suke yi.

Idan muka ga ko muka ji labarin kyawawan hanyoyi, tsaftataccen ruwan sha, sufuri mai inganci da sauran ababen more rayuwa a kasashen duniya, abin da ke fitowa daga bakinmu shi ne “wata miyar sai a makota”.

  • Xi Ya Shiryawa Manyan Baki Liyafar Girmamawa
  • Yadda Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ta Taimaka Wajen Gudanar Da Gasar Cin Kofin Afirka

Amma daga shekarar 2013, yayin da Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”, tunaninmu ya fara sauyawa saboda irin ayyukan raya kasa da shawarar ta fara samarwa a kasashen Afirka.

Egypt, na daga kasashen da suka fara rattaba hannu a shawarar ziri daya da hanya daya a 2013 kuma tuni take cin gajiyar lamarin. Akwai gagarumin aikin gina Sabon Babban Birnin Mulki da kuma yankin masana’antu na Suez Canal da zai yi kafada da kafada da takwarorinsa na duniya. Idan aka kammala gina sabon babban birnin zai rage cunkoso a Cairo, babban birnin kasar na yanzu. Kana yankin masana’antun zai kunshi tashoshin jiragen ruwa shida da masana’antu da cibiyoyin kasuwanci daban-daban da kuma gidajen jama’a.

Ita kuwa Nijeriya wacce ta shiga hadin gwiwar shawarar a 2018 kuma har ila yau a bana take cika shekaru 52 da kulla huldar difilomasiyya da kasar Sin, daga cikin ayyukan more rayuwar da ta ci gajiyarsu, akwai shahararren layin dogon nan da aka shimfida a tsakanin Abuja zuwa Kaduna, da na Babban Birnin Tarayya Abuja, da na Legas zuwa Ibadan. Sai sabbin gine-ginen gudanarwa da tarbar fasinjoji da aka samar a manyan filayen jiragen sama na Kano, Abuja, Legas da Fatakwal. Kana ga tashar teku mai zurfi ta Lekki baya ga wasu ayyukan titunan mota da dama.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Wadannan ayyukan ci gaba sun kawo sauye-sauye masu ma’ana ga rayuwar ‘Yan Nijeriya da dama. Misali, ma’aikatan da ba su da karfin zama a Abuja sun samu saukin zuwa aiki daga Kaduna zuwa Abuja, inda suke zuwa su dawo cikin yini guda.

Haka nan tashar Lekki da ta zama tashar teku mai zurfi mafi girma a Afirka ta Yamma, ana sa rai ta samar da kudin shiga Dala Biliyan 360 da ayyukan yi akalla 170,000.

Bugu da kari, sufurin jiragen kasa da aka kaddamar na cikin Birnin Legas ya taimaka wajen rage cunkoson da ake fama da shi a birnin daga lokacin da aka kaddamar zuwa yanzu, da rage gurbacewar iska a birnin da sauran harkoki na biyan bukatun yau da kullum na ‘yan kasa.

Ba wannan ne ba kadai, akwai sauran ayyuka da dama da Kamfanonin Sin suka gudanar ko suke kan aiwatarwa da ke bayar da gudunmawa ga raya al’umma da tattalin arzikin kasa.

Ba a Nijeriya ne kawai, shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” ke sauya rayuwar al’umma ba da tattalin arzikinsu.

A Kasar Uganda, gina babbar hanyar da ta tashi daga Kampala zuwa Entebbe wacce ta zama ta farko a kasar da ake samun kudin shiga da ita, da madatsun ruwa na samar da wutar lantarki a Karuma da Isimba da aikin fadada Filin Jiragen Sama na Entebbe sun saukaka sha’anin sufuri da bunkasa raya biranen kasar da kuma sada ta da sauran takwarorinta na Afirka, kana da ba da gudunmawa ga habakar tattalin arzikinta.

Haka zalika, a sakamakon “Ziri Daya da Hanya Daya”, ‘yan kasar Senegal da ke fama da matsanancin karancin ruwan sha sun ci gajiyar rijiyoyi na zamani 251 da kasar Sin ta gina inda yanzu haka a kalla mutum miliyan biyu ke amfana, baya ga wasu 3,000 da suka samu aikin yi.

A Angola ma, sama da mutum 600,000 sun amfana da aikin jin kai na Kamfanin Layin Dogo na Kasar Sin (CRCC) wanda ya samar musu da ruwan sha na famfo, karon farko a rayuwarsu.

Tabbas, shawarar Ziri Daya da Hanya Daya ta zama nagge dadi goma, bisa yadda kasashen duniya akalla 152 (zuwa Janairun 2023), na yankin Turai, Asiya da Afirka suka amince tare da yin hadin gwiwa na ci gaba da Kasar Sin a karkashinta.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaKasar SinShawarar ziri daya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ta Taimaka Wajen Gudanar Da Gasar Cin Kofin Afirka

Next Post

Fasinjoji Sun Jikkata Yayin Da Motoci 2 Suka Yi Karo Da Juna A Legas

Related

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

6 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

8 hours ago
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

18 hours ago
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci
Daga Birnin Sin

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

20 hours ago
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

21 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

23 hours ago
Next Post
Fasinjoji Sun Jikkata Yayin Da Motoci 2 Suka Yi Karo Da Juna A Legas

Fasinjoji Sun Jikkata Yayin Da Motoci 2 Suka Yi Karo Da Juna A Legas

LABARAI MASU NASABA

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.