• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya bukaci zababben Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu da ya yi amfani da kwarewarsa wajen magance kalubalen tattalin arzikin da Nijeriya ke fuskanta cikin gaggawa.

Babangida ya bayyana haka ne a ranar Litinin a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Arise TB, inda ya kuma taya Shugaban kasa, Tinubu da mataimakin Shugaban kasa, Kashim Shettima murna rantsar da su da aka yi.

  • Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

Haka kuma IBB ya bayyana Tinubu a matsayin hazikin dan siyasa, yayin da ya bukace shi da ya sake fasalin rundunar sojojin Nijeriya da kuma zaburar da manyan masu karfin tattalin arzikin kasar nan wajen zuwa jari.

“Tinubu kwararren dan siyasa ne wanda ke bukatar yin amfani da basirarsa wajen hada kan al’ummar da ke fama da rikici.
“Dole ne ya zaburar da manyan masu karfin tattalin arzikin Nijeriya na gida da waje, domin magance matsalar tattalin arzikin kasa nan tare da sake fasalin rundunar soji.
“A matsayinsa na babban kwamandan rundunar sojin Nijeriya, akwai bukatar ya sake fasalin rundunonin tsaro ta yadda za a sake farfado da su, da horar da su da kuma sake tsara su yadda ya kamata, saboda akwai babban jan aiki a gaban rundunonin tsaro wajen hada kansu da inganta su,” in ji Babangida.

Babangida ya kuma bukaci ‘yan Nijeriya su yi hakuri da sabuwar gwamnatin Tinubu.
Ya jaddada cewa, Tinubu na bukatar samun damar hada kan Nijeriya, yana mai bayyana ra’ayin cewa akwai mutane masu basira da za su iya taimaka masa wajen gyara kowane fanni ciki har da sojojin kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Babangida ya yi kira ga Tinubu ya zama shugaban kasa ga dukkan ‘yan Nijeriya a daidai lokacin da ya karbi ragamar shugabancin kasar nan.

“Ina yi wa sabuwar gwamnati fatan alheri. Su sanya Nijeriya a gabansu da kuma jin dadin ‘yan Nijeriya, ya kamata wannan ya zama mafi muhimmanci. Shugabanci ya tabarbare a dukkan matakai da ke kasar nan.

“Shawarar kawai ita ce su yi hakuri kuma su ci gaba da tallafa wa sabuwar gwamnati, amma idan sun ga abubuwa suna faruwa ba daidai ba, su yi kokarin yin kira kamar yadda suka saba, amma su kasance masu hakuri game da shugabanci,” in ji Babangida.

Babban jojin Nijeriya, Olukayode Ariwoola ne ya rantsar da Tinubu da Shettima a matsayin shugaban kasa da mataimakinsa.

Mai shari’a Ariwoola ya rantsar da Tinubu da Shettima ne a dandalin Eagles Skuare da ke babban birnin tarayya Abuja a ranar Litinin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

Next Post

Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

Related

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
Labarai

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

2 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

3 hours ago
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara
Labarai

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

5 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

6 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

7 hours ago
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

9 hours ago
Next Post
Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.