ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

Tsohon Shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya bukaci zababben Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu da ya yi amfani da kwarewarsa wajen magance kalubalen tattalin arzikin da Nijeriya ke fuskanta cikin gaggawa.

Babangida ya bayyana haka ne a ranar Litinin a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Arise TB, inda ya kuma taya Shugaban kasa, Tinubu da mataimakin Shugaban kasa, Kashim Shettima murna rantsar da su da aka yi.

  • Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

Haka kuma IBB ya bayyana Tinubu a matsayin hazikin dan siyasa, yayin da ya bukace shi da ya sake fasalin rundunar sojojin Nijeriya da kuma zaburar da manyan masu karfin tattalin arzikin kasar nan wajen zuwa jari.

ADVERTISEMENT

“Tinubu kwararren dan siyasa ne wanda ke bukatar yin amfani da basirarsa wajen hada kan al’ummar da ke fama da rikici.
“Dole ne ya zaburar da manyan masu karfin tattalin arzikin Nijeriya na gida da waje, domin magance matsalar tattalin arzikin kasa nan tare da sake fasalin rundunar soji.
“A matsayinsa na babban kwamandan rundunar sojin Nijeriya, akwai bukatar ya sake fasalin rundunonin tsaro ta yadda za a sake farfado da su, da horar da su da kuma sake tsara su yadda ya kamata, saboda akwai babban jan aiki a gaban rundunonin tsaro wajen hada kansu da inganta su,” in ji Babangida.

Babangida ya kuma bukaci ‘yan Nijeriya su yi hakuri da sabuwar gwamnatin Tinubu.
Ya jaddada cewa, Tinubu na bukatar samun damar hada kan Nijeriya, yana mai bayyana ra’ayin cewa akwai mutane masu basira da za su iya taimaka masa wajen gyara kowane fanni ciki har da sojojin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Babangida ya yi kira ga Tinubu ya zama shugaban kasa ga dukkan ‘yan Nijeriya a daidai lokacin da ya karbi ragamar shugabancin kasar nan.

“Ina yi wa sabuwar gwamnati fatan alheri. Su sanya Nijeriya a gabansu da kuma jin dadin ‘yan Nijeriya, ya kamata wannan ya zama mafi muhimmanci. Shugabanci ya tabarbare a dukkan matakai da ke kasar nan.

“Shawarar kawai ita ce su yi hakuri kuma su ci gaba da tallafa wa sabuwar gwamnati, amma idan sun ga abubuwa suna faruwa ba daidai ba, su yi kokarin yin kira kamar yadda suka saba, amma su kasance masu hakuri game da shugabanci,” in ji Babangida.

Babban jojin Nijeriya, Olukayode Ariwoola ne ya rantsar da Tinubu da Shettima a matsayin shugaban kasa da mataimakinsa.

Mai shari’a Ariwoola ya rantsar da Tinubu da Shettima ne a dandalin Eagles Skuare da ke babban birnin tarayya Abuja a ranar Litinin.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.