• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekarar 2024: Kyautata Fata A Cikin Duniyar Kalubale

by CGTN Hausa
2 years ago
2024

A cikin sarkakiyar yanayin siyasar kasa da kasa, da jerin kalubalen da ke fuskantar bil’Adam wandada ba kasafai za a shawo kansu ba, akwai kyakkyawar fata da kuma ci gaba yayin da muka shigo cikin shekarar 2024. Duk da rikice-rikicen Gabas ta Tsakiya, da gwagwarmayar shugabancin duniya tsakanin kasashen yamma da sauran kasashen duniya, da rikice-rikicen sauyin yanayi, da sauran batutuwan da suka mamaye kanun labarai a shekarar 2023, yana da muhimmanci mu waiwayi ci gaban da bil’Adama suka samu ta hanyar hadin kai, da ci gaban sabbin fasahohi musamman na zamani, da yunkurin diflomasiyya, da binciken sararin samaniya, wadanda suka ba da gudummawa ga kyakkyawar labarin ci gaba da burin bai daya na bil’Adama a shekarar bara, shi ya sa muke kyautata zaton shigowa shekarar 2024 da kafar dama.

Cudanya da mu’amala da muke yi da juna suna ba da damammaki ga hadin gwiwa, da fahimta, da warware matsaloli na gama gari. Ta hanyar mai da hankali kan wadannan abubuwa masu kyau, za mu iya yin aiki don gina makomar da ke nuna mafi kyawun damammaki ga bil’Adam, wato makomar da ke da alaka da hadin kai, kirkira da sadaukar da kai ga raya zamantakewar al’ummarmu.

  • Burin Sin Na Kara Jin Dadin Zaman Jama’a Ya Dace Da Begen Jama’ar Kasa Da Kasa
  • Xi Da Kim Sun Ayyana Shekarar 2024 A Matsayin Shekarar Abokantaka Tsakanin Sin Da Koriya Ta Arewa

An samu munanan rikice-rikice na kasa da kasa da suka barke a cikin 2023, daga yakin da aka dade ana tafkawa tsakanin Rasha da Ukraine zuwa rikicin baya-bayan nan a zirin Gaza, ba sai na ambato yawan tsokanar da Amurka ke yi a tekun kudancin kasar Sin ba, wadanda suka haifar da a kalla illoli guda biyu masu lahani ga tattalin arzikin duniya. Na farkon ya zo daidai da yunkurin da Amurka ke yi na bata tsarin samar da kayayyaki a duniya ta hanyar amfani da jadawalin kudin fito, da haraji, da takunkumi. Na biyun shi ne sakamakon zagon kasar da Amurka ke yi da na ambato, ya haifar da wani sabon yakin cacar baki, wanda ke da illa ga ci gaban tattalin arzikin duniya da kuma jin dadin rayuwar bil’Adam tare da makomar bai daya.

A taron kolin tattalin arzikin kasar Sin da aka gudanar a ranakun 11 da 12 ga watar Disamban shekarar da ta shude a nan birnin Beijing, shugabannin kasar Sin su yanke shawarwari kan muhimman batutuwan da suka shafi harkokin tattalin arziki a shekarar 2024. A gun taron, an bayyana cewa, tattalin arzikin kasar Sin ya samu farfadowa, tare da samun ci gaba mai inganci. A dunkule, yanayi mai kyau ya zarce kalubaloli game da ci gaban kasar Sin, kuma tushen tsarin farfado da tattalin arziki da kyakkyawan hangen nesa na dogon lokaci bai canza ba.

A duk halin da ake ciki dai, kasar Sin za ta yi iya kokarinta wajen samar da tsare-tsare da kuma tuntuba da tattaunawa domin kara fahimtar muradun bai daya. Ba za ta nemi kasashen duniya da su rarrabu ba, akasin haka, za ta kiyaye ingancin tsarin samar da kayayyaki na duniya da sunan kyautata jin dadin jama’a kan karin kariyar ga kasashen duniya.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Shugaban kasar Sin Xi Jinping a cikin jawabinsa na murnar sabuwar shekara ya ce, “al’ummar Sinawa na dora matukar muhimmanci ga zaman lafiya. Muna fatan za mu hada kai da daukacin kasashen duniya. Ya kamata mu yi la’akari da makoma da jin dadin bil’Adam. Ya kamata mu kara azama kan raya kyakkyawar makomar bai daya ta bil’Adama da gina duniyarmu da kowa zai ji dadin zama a cikinta”. (Yahaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani
Daga Birnin Sin

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Next Post
Goron Barka Da Shiga Sabuwar Shekarar 2024 Daga Jawabin Shugaban kasar Sin

Goron Barka Da Shiga Sabuwar Shekarar 2024 Daga Jawabin Shugaban kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
2024

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.