ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Burin Sin Na Kara Jin Dadin Zaman Jama’a Ya Dace Da Begen Jama’ar Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Shekarar da ta gabata, shekara ce da bunkasuwar tattalin arzikin Sin ya farfado, bayan ta kyautata matakan dakile da kandagarkin cutar COVID-19, wadanda ta dauki shekaru 3 tana gudanar da su. Ko da yake an fuskanci matsaloli da dama, amma dukkan Sinawa sun yi kokari don ba da gudummawarsu.

Kamar yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya fada a cikin jawabinsa na murnar sabuwar shekarar 2024, wato “Muna da babban burin da muke fatan cimmawa, burin da ke shafar kowa, wato za mu yi kokarin ganin al’ummar Sinawa na kara jin dadin zaman rayuwarsu”. Kara jin dadin zaman rayuwa shi ne babban burin kasar Sin, kana ya dace da begen jama’ar duniya baki daya.

  • Shugabannin Sin Da Rasha Sun Tura Wa Juna Sakwanni Don Murnar Sabuwar Shekara
  • Xi Da Biden Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 45 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu

Idan ana son jama’ar duniya su kara jin dadin zaman rayuwa, da farko ana bukatar zaman lafiya da kwanciyar hankali. Kasar Sin ta yi kokari wajen gabatar da ra’ayinta kan daidaita rikicin Ukraine ta hanyar siyasa, da takardar daidaita rikicin dake tsakanin Palesdinu da Isra’ila, da tura jami’ai da dama don shiga tsakani kan daidaita rikicin, wanda ya samu amincewa daga kasa da kasa.

ADVERTISEMENT

Bunkasuwa shi ne mabudin daidaita dukkan matsaloli. A cikin manyan kasashe masu karfin tattalin arziki a duniya, tattalin arzikin Sin ya karu da kashi 5.2 cikin 100 a rubu’i uku na farkon shekarar 2023 bisa na makamancin lokacin shekarar 2022, Sin ta kiyaye matsayinta na kasa mafi bayar da gudummawa ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya. Kana Sin ta kafa dandalin hadin gwiwa da dama don more damar samun bunkasuwa tare da kasashen duniya.

Jama’a a fadin duniya suna rayuwa mai kyau, kuma suna fatan samun karin adalci a harkokin duniya. An gudanar da taron kolin Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya, da dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya karo na uku, da shigar da sabbin membobi a cikin BRICS, da ganawa a tsakanin shugabannin Sin da Amurka a San Francisco, kasar Sin ta yi kokarin kiyaye tsarin kasa da kasa, da raya karfin kasashe masu tasowa, da kuma ba da tabbaci da kwanciyar hankali ga duniyar dake fuskantar sauye-sauye da rikici.

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

A yayin da aka shiga sabuwar shekara, ba ma kawai Sin tana tunanin kanta kadai ba, har ma da duniya baki daya. A shekarar 2024, kasar Sin tana son hada kai da kasashen duniya wajen tinkarar kalubale da sa kaimi ga samun wadata tare. (Zainab Zhang)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
Sarkin Kano

Za Mu Cigaba Da Fadakarwa Kan Dorewar  Zaman Lafiya Tsakanin Arewa Da Kudu – Sarkin Kano

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.