• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekarar “Zomo” Dake Samar Da Yanayi Mai Armashi

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shekarar “Zomo” Dake Samar Da Yanayi Mai Armashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wadannan kwanaki, Sinawa suna murnar bikin sabuwar shekara ta gargajiyarsu, wanda ake kira “bikin bazara”. Don taya murnar bikin, wani abokina dake Kano ya buga mana waya a jiya. Ya fahimci al’adun kasar Sin sosai, don haka ya san Sinawa na yin amfani da zagayowar wasu dabbobi 12, wajen wakiltar shekaru daban daban. Ya ce mana: “Ina taya Sinawa murnar sabuwar shekara ta Zomo, da fatan kowa zai kasance cikin koshin lafiya, da iya gudu cikin sauri, kamar yadda zomo yake.”

Ina godiya sosai bisa fatan alheri da aka yi mana, kana na ga wasu abubuwa suna “gudu cikin sauri” a nan kasar Sin, kamar dai yadda wannan aboki ya fada.

  • Ko Kun San Irin Bakar Wuyar Da Ake Sha Wajen Tantance Gawarwaki A Yakin Ukraine?

Da farko, annobar COVID-19 nau’in Omicron na “gudu”, inda ake sa ran ganin bayanta cikin sauri a nan kasar Sin.

Bisa alkaluman da cibiyar kandagarkin cututtuka ta kasar Sin ta bayar, an ce an samu mafi yawan mutanen da suka nemi samun jinya a asibiti a kewayen ranar 22 ga watan Disamban bara, inda yawansu ya kai miliyan 2 da dubu 867 a duk rana. Daga baya jimillar ta fara raguwa. Zuwa ranar 23 ga watan da muke ciki, jimillar ta sauka zuwa dubu 110, wato ta ragu da kashi 96.2%.

Kar mu manta, ana samun mafi yawan zirga-zirgar mutane a lokacin bikin bazara a kasar Sin, musamman ma ta la’akari da yadda kasar ta sassauta matakan kandagarkin yaduwar cutar COVID tun daga karshen bara, inda ko a ranar 24 ga wata kadai, aka samu fasinjoji fiye da miliyan 29 da suka yi zirga-zirga a kasar, adadin da ya karu da kashi 67.3% bisa makamancin lokacin bara. Amma duk da haka, kwararar mutane ba ta tsananta yanayin bazuwar COVID ba. Hakan ya nuna cewa, matakan hana yaduwar annoba da aka daidaita su, sun yi amfani.

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Na biyu shi ne, bayan da yanayin annoba ya yi sauki, tattalin arziki ma na farfadowa cikin karin sauri.

A wadannan kwanaki, na ziyarci cibiyoyin kasuwanci na Beijing, da wuraren cin abinci, da kallon sinima, da sauran nune-nune, inda na ga ko ina na cike da mutane, kana suna kokarin sayayya da kashe kudi. Alkaluman da hukumar kasuwanci ta birnin Beijing ta gabatar sun nuna cewa, daga ranar 21 zuwa ta 24 ga wata, wato cikin kwanaki 4 kacal, darajar kayayyaki da abinci da aka sayar da su a birnin Beijing ta kai Yuan biliyan 2.84, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 420.

Kana wannan yanayi mai armashi ya bazu a wurare daban daban. Bisa abun da na gani a telabijin, a duk wani gari na kasar Sin, ana samun cunkuson mutane a wuraren shakatawa, inda ‘yan kasuwa ke shan aiki, suna farin ciki bisa dimbin ribar da suka samu. To, yadda aka samu farawar sabuwar shekara kamar haka, ya nuna yadda tattalin arzikin kasar zai samu ci gaba cikin karin sauri a wannan shekarar da muke ciki.

Har yanzu ban manta da bikin bazara na shekaru 3 da suka wuce ba. Inda a ranar 23 ga watan Janairun shekarar 2020, birnin Wuhan da aka samu barkewar annobar COVID-19 a cikin sa, ya sanar da killace kansa, kana wurare daban daban na kasar Sin suka fara tura mutane da kayayyakin da ake bukata zuwa birnin don ba shi taimako. A lokacin, na soke shirin ziyara, inda ni da iyali na muka kasance a gida don magance kamuwa da cuta.

Sa’an nan a shekaru 2 da suka biyo baya, an ci gaba da daukar tsauraran matakan kandagarkin cuta a nan kasar Sin. Inda mutanen kasar suka yi kokarin hana yaduwar cutar COVID-19, bisa hadin gwiwa, da da’a, da jajircewa, don kare rayukan jama’a daga mummunar cutar mai kisa. Ana ci gaba da wannan kokari, har zuwa karshen shekarar bara, lokacin da aka samu cikar sharudan sassauta matakan kandagarkin cuta.

Saboda haka a wannan bikin bazara, Sinawa sun samu cikakkiyar damar jin dadin haduwa da iyalai, da ziyara a wurare daban daban. Sai dai an fi samun sauyawa cikin zukatansu, inda tsoron kamuwa da cuta ya ragu sosai, kana imani game da makoma mai haske ya karfafa.

Burina shi ne, wannan imani na Sinawa zai taimakawa karfafa gwiwar mutanen kasashe daban daban, kana ci gaban tattalin arzikin Sin zai sa tattalin arzikin duniya samun farfadowa cikin matukar sauri, har ma ya fi saurin gudu na zomo, a wannan shekara ta zomo da muke ciki. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kaso Mai Tsoka Na Ra’ayoyin Jama’a Ya Nuna Gamsuwa Da Nasarar Kasar Sin A Fannin Kandagarkin COVID-19

Next Post

2023: INEC Da ‘Yansanda Sun Nanata Kudirin Samun Sahihin Zabe

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

2 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

4 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

4 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

8 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

10 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

10 hours ago
Next Post
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

2023: INEC Da 'Yansanda Sun Nanata Kudirin Samun Sahihin Zabe

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.