ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: INEC Da ‘Yansanda Sun Nanata Kudirin Samun Sahihin Zabe

by Sulaiman
4 years ago
INEC

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) da rundunonin ‘yan sanda na jihohin Edo, Delta da Bayelsa sun bayyana cewa sun kammala dukkan wani shiri domin gudanar da manyan zaɓuɓɓukan shekarar 2023 ba tare da wani cikas ba.

 

Zaunannun Kwamishinonin Zaɓe na INEC (REC) da ke waɗannan jihohin su ne su ka bayyana haka a hirarrakin da su ka yi a lokuta daban-daban da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN).

ADVERTISEMENT
  • INEC Ta Gargadi Jami’anta Kan Karbar Na Goro Daga Masu Karbar Katin Zabe

A cewar su, ƙarin hare-haren ta’addanci da ake kai ofisoshi da kayan aikin su a faɗin ƙasar nan bai sa sun karaya ba kan ƙudirin su.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Mista Monday Udoh-Tom, wanda shi ne Kwamishinan Zaɓen INEC a Delta, a yayin da ya ke bayyana cewa hukumar ta gama shirya wa zaɓen, ya yi bayanin cewa sun gama dukkan tsare-tsaren da su ka kamata don tabbatar da cewa an yi zaɓe cikin lumana.

 

Ya ce: ”A cikin watanni takwas da su ka gabata zuwa yau INEC ta yi gagarumin aikin wayar da kan jama’a, domin tabbatar da cewa an gudanar da zaɓe sahihi, karɓaɓɓe kuma a cikin adalci.

 

 

”Daga cikin ayyukan da hukumar ta gudanar akwai aikin sabunta rajista da kuma karɓar katin shaidar rajistar zaɓe wanda ake kan ci gaba da karɓa a yanzu haka.

 

Utom ya ce INEC ta riƙa tuntuɓar ƙungiyoyi, hukumomin tsaro, kafafen yaɗa labarai da sauran masu ruwa da tsaki a harkokin gudanar da zaɓe domin zaburarwa zuwa ga gaggauta shirye-shiryen gudanar da zaɓe.

 

Ya ce INEC ba za ta miƙa wuya ga duk wata barazana ba, don haka sai ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki su bai wa hukumar goyon baya domin tabbatar da an yi zaɓe lami lafiya a cikin kwanciyar hankali.

 

 

Ba za mu bari a yi cuwa-cuwar cinikin ƙuri’u ba – Rundunar ‘Yan Sanda:

 

Dangane da irin tanade-tanaden da ta yi a fannin tsaro, Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Edo ta ce ta daɗe da yin shiri domin ganin cewa an yi zaɓe a cikin kwanciyar hankali a Jihar Edo.

 

Kwamishinan ‘Yan Sanda Mohammed Ɗanƙwara, ya ce sun fito da wani shirin samar da cikakken tsaro, wanda su ka raɗa wa suna ‘Operation Order’, wanda ya ce gaba ɗayan ‘yan sandan jihar kowa na ciki.

 

Ɗanƙwara wanda Kakakin Yaɗa Labaran ‘yan sandan Edo, Chidi Nwabuizor ya wakilta, ya ce a zaɓen 2023 masu sayen ƙuri’u da dillalan su ba za su ci kasuwa ba.

 

“Ba za mu gani, ko mu ji labarin ana cuwa-cuwar cinikin ƙuri’u a ranar zaɓe ba,” inji shi.

 

Su ma kwamishinonin ‘yan sandan jihohin Delta da Bayelsa sun bayyana irin na su shirye-shiryen da su ka yi, domin tabbatar da samar da tsaro, wanda hakan zai sa a gudanar da zaɓukan 2023 cikin kwanciyar hankali.

INEC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Matar Aure Ta Bukaci Kotu Ta Raba Aurenta Da Mijinta Kan Rashin Kulawa

Matar Aure Ta Bukaci Kotu Ta Raba Aurenta Da Mijinta Kan Rashin Kulawa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.