ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: INEC Da ‘Yansanda Sun Nanata Kudirin Samun Sahihin Zabe

by Sulaiman
3 years ago
INEC

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) da rundunonin ‘yan sanda na jihohin Edo, Delta da Bayelsa sun bayyana cewa sun kammala dukkan wani shiri domin gudanar da manyan zaɓuɓɓukan shekarar 2023 ba tare da wani cikas ba.

 

Zaunannun Kwamishinonin Zaɓe na INEC (REC) da ke waɗannan jihohin su ne su ka bayyana haka a hirarrakin da su ka yi a lokuta daban-daban da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN).

ADVERTISEMENT
  • INEC Ta Gargadi Jami’anta Kan Karbar Na Goro Daga Masu Karbar Katin Zabe

A cewar su, ƙarin hare-haren ta’addanci da ake kai ofisoshi da kayan aikin su a faɗin ƙasar nan bai sa sun karaya ba kan ƙudirin su.

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Mista Monday Udoh-Tom, wanda shi ne Kwamishinan Zaɓen INEC a Delta, a yayin da ya ke bayyana cewa hukumar ta gama shirya wa zaɓen, ya yi bayanin cewa sun gama dukkan tsare-tsaren da su ka kamata don tabbatar da cewa an yi zaɓe cikin lumana.

 

Ya ce: ”A cikin watanni takwas da su ka gabata zuwa yau INEC ta yi gagarumin aikin wayar da kan jama’a, domin tabbatar da cewa an gudanar da zaɓe sahihi, karɓaɓɓe kuma a cikin adalci.

 

 

”Daga cikin ayyukan da hukumar ta gudanar akwai aikin sabunta rajista da kuma karɓar katin shaidar rajistar zaɓe wanda ake kan ci gaba da karɓa a yanzu haka.

 

Utom ya ce INEC ta riƙa tuntuɓar ƙungiyoyi, hukumomin tsaro, kafafen yaɗa labarai da sauran masu ruwa da tsaki a harkokin gudanar da zaɓe domin zaburarwa zuwa ga gaggauta shirye-shiryen gudanar da zaɓe.

 

Ya ce INEC ba za ta miƙa wuya ga duk wata barazana ba, don haka sai ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki su bai wa hukumar goyon baya domin tabbatar da an yi zaɓe lami lafiya a cikin kwanciyar hankali.

 

 

Ba za mu bari a yi cuwa-cuwar cinikin ƙuri’u ba – Rundunar ‘Yan Sanda:

 

Dangane da irin tanade-tanaden da ta yi a fannin tsaro, Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Edo ta ce ta daɗe da yin shiri domin ganin cewa an yi zaɓe a cikin kwanciyar hankali a Jihar Edo.

 

Kwamishinan ‘Yan Sanda Mohammed Ɗanƙwara, ya ce sun fito da wani shirin samar da cikakken tsaro, wanda su ka raɗa wa suna ‘Operation Order’, wanda ya ce gaba ɗayan ‘yan sandan jihar kowa na ciki.

 

Ɗanƙwara wanda Kakakin Yaɗa Labaran ‘yan sandan Edo, Chidi Nwabuizor ya wakilta, ya ce a zaɓen 2023 masu sayen ƙuri’u da dillalan su ba za su ci kasuwa ba.

 

“Ba za mu gani, ko mu ji labarin ana cuwa-cuwar cinikin ƙuri’u a ranar zaɓe ba,” inji shi.

 

Su ma kwamishinonin ‘yan sandan jihohin Delta da Bayelsa sun bayyana irin na su shirye-shiryen da su ka yi, domin tabbatar da samar da tsaro, wanda hakan zai sa a gudanar da zaɓukan 2023 cikin kwanciyar hankali.

INEC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Matar Aure Ta Bukaci Kotu Ta Raba Aurenta Da Mijinta Kan Rashin Kulawa

Matar Aure Ta Bukaci Kotu Ta Raba Aurenta Da Mijinta Kan Rashin Kulawa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.