ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: INEC Da ‘Yansanda Sun Nanata Kudirin Samun Sahihin Zabe

by Sulaiman
3 years ago
INEC

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) da rundunonin ‘yan sanda na jihohin Edo, Delta da Bayelsa sun bayyana cewa sun kammala dukkan wani shiri domin gudanar da manyan zaɓuɓɓukan shekarar 2023 ba tare da wani cikas ba.

 

Zaunannun Kwamishinonin Zaɓe na INEC (REC) da ke waɗannan jihohin su ne su ka bayyana haka a hirarrakin da su ka yi a lokuta daban-daban da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN).

ADVERTISEMENT
  • INEC Ta Gargadi Jami’anta Kan Karbar Na Goro Daga Masu Karbar Katin Zabe

A cewar su, ƙarin hare-haren ta’addanci da ake kai ofisoshi da kayan aikin su a faɗin ƙasar nan bai sa sun karaya ba kan ƙudirin su.

 

LABARAI MASU NASABA

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Mista Monday Udoh-Tom, wanda shi ne Kwamishinan Zaɓen INEC a Delta, a yayin da ya ke bayyana cewa hukumar ta gama shirya wa zaɓen, ya yi bayanin cewa sun gama dukkan tsare-tsaren da su ka kamata don tabbatar da cewa an yi zaɓe cikin lumana.

 

Ya ce: ”A cikin watanni takwas da su ka gabata zuwa yau INEC ta yi gagarumin aikin wayar da kan jama’a, domin tabbatar da cewa an gudanar da zaɓe sahihi, karɓaɓɓe kuma a cikin adalci.

 

 

”Daga cikin ayyukan da hukumar ta gudanar akwai aikin sabunta rajista da kuma karɓar katin shaidar rajistar zaɓe wanda ake kan ci gaba da karɓa a yanzu haka.

 

Utom ya ce INEC ta riƙa tuntuɓar ƙungiyoyi, hukumomin tsaro, kafafen yaɗa labarai da sauran masu ruwa da tsaki a harkokin gudanar da zaɓe domin zaburarwa zuwa ga gaggauta shirye-shiryen gudanar da zaɓe.

 

Ya ce INEC ba za ta miƙa wuya ga duk wata barazana ba, don haka sai ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki su bai wa hukumar goyon baya domin tabbatar da an yi zaɓe lami lafiya a cikin kwanciyar hankali.

 

 

Ba za mu bari a yi cuwa-cuwar cinikin ƙuri’u ba – Rundunar ‘Yan Sanda:

 

Dangane da irin tanade-tanaden da ta yi a fannin tsaro, Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Edo ta ce ta daɗe da yin shiri domin ganin cewa an yi zaɓe a cikin kwanciyar hankali a Jihar Edo.

 

Kwamishinan ‘Yan Sanda Mohammed Ɗanƙwara, ya ce sun fito da wani shirin samar da cikakken tsaro, wanda su ka raɗa wa suna ‘Operation Order’, wanda ya ce gaba ɗayan ‘yan sandan jihar kowa na ciki.

 

Ɗanƙwara wanda Kakakin Yaɗa Labaran ‘yan sandan Edo, Chidi Nwabuizor ya wakilta, ya ce a zaɓen 2023 masu sayen ƙuri’u da dillalan su ba za su ci kasuwa ba.

 

“Ba za mu gani, ko mu ji labarin ana cuwa-cuwar cinikin ƙuri’u a ranar zaɓe ba,” inji shi.

 

Su ma kwamishinonin ‘yan sandan jihohin Delta da Bayelsa sun bayyana irin na su shirye-shiryen da su ka yi, domin tabbatar da samar da tsaro, wanda hakan zai sa a gudanar da zaɓukan 2023 cikin kwanciyar hankali.

INEC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026
  • Sulaiman
    Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa
  • Sulaiman
    Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

MASU ALAKA

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
Labarai

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala
Labarai

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Next Post
Matar Aure Ta Bukaci Kotu Ta Raba Aurenta Da Mijinta Kan Rashin Kulawa

Matar Aure Ta Bukaci Kotu Ta Raba Aurenta Da Mijinta Kan Rashin Kulawa

LABARAI MASU NASABA

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.