• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shettima Zai Kaddamar Da Cibiyar Horaswa Da zaƙulo Hazikan Matasa A Gombe

Shirin Guraben Ayyuka 2,000 Ga Matasa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Shettima Zai Kaddamar Da Cibiyar Horaswa Da zaƙulo Hazikan Matasa A Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jihar Gombe ta shirya karɓar baƙuncin Mataimakin Shugaban Nijeriya, Sanata Kashim Shettima, a ranar Litinin inda zai ƙaddamar da shirin samar da guraben ayyuka da janyo masu zuba jari daga waje (OTNI) tare da ƙaddamar da Cibiyar Horaswa da zaƙulo Hazikan Matasa (BPO). 

Cibiyar ta BPO wacce ita ce ta farko a shiyyar Arewa Maso Gabas kuma irinta mafi girma a Nijeriya, an tsara zata samar da aƙalla guraben ayyukan yi 2,000 ga matasa masu basira da hazaƙa a Jihar Gombe bisa irin jagorancin hangen nesa na Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya.

  • Tsokaci Kan Yadda Matsin Rayuwa Ke Sa Wasu Mata Da ‘Yan Mata Aikata Fasadi
  • Gwamnatin Kano Na Shirin Dawo Da Sheikh Daurawa Kujerarsa Ta Hisba

Yanzu da aka kafa cibiyar ta BPO a Gombe, a Cibiyar Horar da Sana’o’i ta Amina Mohammed Skills Acquisition Centre da ke Bypass daura da hanyar Gombe zuwa Biu, jihar ta shirya zama cibiyar samar da kayayyaki, ta hanyar amfani da basira da hazakar matasanta.

Cibiya irin ta OTNI, hanya ce dake kawo sauyi a harkar kasuwanci da samar da fasahar ƙere-ƙere, kuma hanya ce mafi sauri da za ta samar da ayyukan yi ga matasan Jihar Gombe dama Nijeriya baki ɗaya.

A cewar sanarwar da Ismaila Uba Misilli, Babban Daraktan Yaɗa Labarun Gwamnan Jihar Gombe ya fitar, ta hanyar shiga wannan shiri, gwamnatin Gwamna Inuwa Yahaya ta ƙara nuna aniyarta na samar da ayyukan yi masu ɗorewa da baiwa matasa damar bada gudumawa mai ma’ana ga ci gaban jihar.

Labarai Masu Nasaba

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

Misilli ya ce, “Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya yana miƙa godiya ga Mai Girma Mataimakin Shugaban Ƙasan Kashim Shettima bisa goyon baya da jajircewansa wajen bunƙasa tattalin arzikin Jihar Gombe dama Nijeriya baki ɗaya, a daidai lokacin da yake shirin karɓar baƙuncin mataimakin shugaban ƙasan da sauran baƙi.”

“Taron ƙaddamarwar zai gudana ne a ɗakin taro na ƙasa da ƙasa dake kan hanyar Gombe zuwa Bauchi da misalin ƙarfe 9:00 na safe, wanda zai samu halartar manyan masu ruwa da tsaki na gwamnati da masu zaman kansu daga ciki da wajen kasar nan.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cibiyoyin horas da MatasaSabuwar fasahar kirkire-kirkireSabuwar jihar Gombe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Sa Amurka Ke Jin “Tsoron” Kasar Sin Har Da Na’urar Daga Kaya Da Ta Samar?

Next Post

Ramadan: Sanata Abdulaziz Yari Zai Raba Tirela 358 Na Kayan Abinci A Jihar Zamfara

Related

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya
Labarai

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

1 hour ago
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa
Labarai

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

2 hours ago
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

4 hours ago
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku
Labarai

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

4 hours ago
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 
Labarai

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

8 hours ago
Next Post
Ramadan: Sanata Abdulaziz Yari Zai Raba Tirela 358 Na Kayan Abinci A Jihar Zamfara

Ramadan: Sanata Abdulaziz Yari Zai Raba Tirela 358 Na Kayan Abinci A Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

October 5, 2025
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

October 5, 2025
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.