• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Amurka Za Ta Cika Alkawurranta A Wannan Karon?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shin Amurka Za Ta Cika Alkawurranta A Wannan Karon?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ziyarar sakatariyar harkokin cinikayya na Amurka Gina Raimondo a kasar Sin, tana ci gaba da daukar hankalin kafafen yada labarai, inda ake bayyana mabambantan ra’ayoyi.

Tuni dai muka riga mu kan san cewa, Amurka ce ta fara kaddamarwa tare da ci gaba da rura yakin cinikayya tsakaninta da Sin. Sai dai, bisa dukkan alamu kamar yadda aka yi hasashe, ita ce ta fi jin radadin matakan a jikinta. Misali, a cewar sakatariya Gina Raimondo, idan Sin ta koma matakin da take a shekarar 2019 a bangaren yawo bude ido kadai, to hakan zai karawa Amurkar dala biliyan 30 cikin tattalin arzikinta tare da samar da guraben ayyukan yi sama da 50,000.

  • Daga watan Janairu zuwa Yuli, kudaden shigar kasuwancin software na kasar Sin ya karu da 13.6%

Da alamu irin dimbin alfanun da kasar Sin za ta kawo mata ne ya sa take son kyautata hulda tsakaninta da Sin musamman ta fuskar cinikayya, ganin yadda ta soke jerin sunayen wasu kamfanonin Sin da a baya ta sanyawa takunkumai, gabanin ziyarar madam Raimondo.

Cikin lokaci mai tsawo, kasar Sin ta jajirce wajen raya kanta tare da zama mai matukar muhimmanci ta fuskar samar da kayayyaki da cinikayya da ma jagorantar bangarorin kere-kere daban-daban, lamarin da ya sanya ta zama wani bangare mai matukar muhimmanci ga kamfanonin kasashen waje, ciki har da na Amurka.

A ganina, yadda kasar Sin ke ci gaba da samun habakar tattalin arziki, da kuma yadda Amurka ke jin radadin illolin matakanta, sun tilastawa Amurka neman kyautata huldarta da kasar Sin, bisa la’akari da yadda jami’anta ke ci gaba da kawo ziyara kasar.

Labarai Masu Nasaba

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Kamar yadda bangarorin biyu suka bayyana, za su kyautata tuntubar juna a tsakaninsu domin a rika tattaunawa a kai a kai. Ko shakka babu, rashin fahimta na daya daga cikin matsalolin da a kan samu a dangantakar manyan kasashen biyu. Don haka, tuntubar juna zai taka muhimmiyar rawa wajen fahimtar manufofi da dabarun juna.

Duk da cewa Amurka na nuna kudurinta na son kyautata hulda tsakaninta da kasar Sin, ta kan kuma aiwatar da abubuwan da su kan saba da huldar kasa da kasa. Amurka ta fi mayar da hankali ne kan ribar da za ta samu ko da kuwa daya bangaren zai yi asara, yayin da kasar Sin ke neman moriyar juna domin a gudu tare a tsira tare. Shawara dai ya ragewa Amurka, ko ta cika alkawuran da ta dauka da girmama alakarta da Sin, ko ta ci gaba da dandana kudarta. (Faeza Mustapha)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS Ta Bude Ofishin Samar Da Ingantaccen Fasfo A Zariya

Next Post

Babu Kasar Da Za Ta Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tabbatuwar Tsaro Ba

Related

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu
Daga Birnin Sin

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

17 hours ago
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

18 hours ago
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar
Daga Birnin Sin

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

19 hours ago
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

2 days ago
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
Daga Birnin Sin

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

2 days ago
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
Daga Birnin Sin

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

2 days ago
Next Post
Babu Kasar Da Za Ta Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tabbatuwar Tsaro Ba

Babu Kasar Da Za Ta Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tabbatuwar Tsaro Ba

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

August 4, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

August 4, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

August 4, 2025
Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

August 4, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.