• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Amurka Za Ta Cika Alkawurranta A Wannan Karon?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shin Amurka Za Ta Cika Alkawurranta A Wannan Karon?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ziyarar sakatariyar harkokin cinikayya na Amurka Gina Raimondo a kasar Sin, tana ci gaba da daukar hankalin kafafen yada labarai, inda ake bayyana mabambantan ra’ayoyi.

Tuni dai muka riga mu kan san cewa, Amurka ce ta fara kaddamarwa tare da ci gaba da rura yakin cinikayya tsakaninta da Sin. Sai dai, bisa dukkan alamu kamar yadda aka yi hasashe, ita ce ta fi jin radadin matakan a jikinta. Misali, a cewar sakatariya Gina Raimondo, idan Sin ta koma matakin da take a shekarar 2019 a bangaren yawo bude ido kadai, to hakan zai karawa Amurkar dala biliyan 30 cikin tattalin arzikinta tare da samar da guraben ayyukan yi sama da 50,000.

  • Daga watan Janairu zuwa Yuli, kudaden shigar kasuwancin software na kasar Sin ya karu da 13.6%

Da alamu irin dimbin alfanun da kasar Sin za ta kawo mata ne ya sa take son kyautata hulda tsakaninta da Sin musamman ta fuskar cinikayya, ganin yadda ta soke jerin sunayen wasu kamfanonin Sin da a baya ta sanyawa takunkumai, gabanin ziyarar madam Raimondo.

Cikin lokaci mai tsawo, kasar Sin ta jajirce wajen raya kanta tare da zama mai matukar muhimmanci ta fuskar samar da kayayyaki da cinikayya da ma jagorantar bangarorin kere-kere daban-daban, lamarin da ya sanya ta zama wani bangare mai matukar muhimmanci ga kamfanonin kasashen waje, ciki har da na Amurka.

A ganina, yadda kasar Sin ke ci gaba da samun habakar tattalin arziki, da kuma yadda Amurka ke jin radadin illolin matakanta, sun tilastawa Amurka neman kyautata huldarta da kasar Sin, bisa la’akari da yadda jami’anta ke ci gaba da kawo ziyara kasar.

Labarai Masu Nasaba

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Kamar yadda bangarorin biyu suka bayyana, za su kyautata tuntubar juna a tsakaninsu domin a rika tattaunawa a kai a kai. Ko shakka babu, rashin fahimta na daya daga cikin matsalolin da a kan samu a dangantakar manyan kasashen biyu. Don haka, tuntubar juna zai taka muhimmiyar rawa wajen fahimtar manufofi da dabarun juna.

Duk da cewa Amurka na nuna kudurinta na son kyautata hulda tsakaninta da kasar Sin, ta kan kuma aiwatar da abubuwan da su kan saba da huldar kasa da kasa. Amurka ta fi mayar da hankali ne kan ribar da za ta samu ko da kuwa daya bangaren zai yi asara, yayin da kasar Sin ke neman moriyar juna domin a gudu tare a tsira tare. Shawara dai ya ragewa Amurka, ko ta cika alkawuran da ta dauka da girmama alakarta da Sin, ko ta ci gaba da dandana kudarta. (Faeza Mustapha)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS Ta Bude Ofishin Samar Da Ingantaccen Fasfo A Zariya

Next Post

Babu Kasar Da Za Ta Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tabbatuwar Tsaro Ba

Related

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai
Daga Birnin Sin

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

17 hours ago
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

18 hours ago
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

19 hours ago
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

21 hours ago
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 
Daga Birnin Sin

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

23 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

1 day ago
Next Post
Babu Kasar Da Za Ta Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tabbatuwar Tsaro Ba

Babu Kasar Da Za Ta Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tabbatuwar Tsaro Ba

LABARAI MASU NASABA

Hukumar kashe gobara

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

June 5, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

June 5, 2025
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

June 5, 2025
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

June 5, 2025
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

June 5, 2025
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

June 5, 2025
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

June 5, 2025
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.