• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Amurka Za Ta Cika Alkawurranta A Wannan Karon?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shin Amurka Za Ta Cika Alkawurranta A Wannan Karon?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ziyarar sakatariyar harkokin cinikayya na Amurka Gina Raimondo a kasar Sin, tana ci gaba da daukar hankalin kafafen yada labarai, inda ake bayyana mabambantan ra’ayoyi.

Tuni dai muka riga mu kan san cewa, Amurka ce ta fara kaddamarwa tare da ci gaba da rura yakin cinikayya tsakaninta da Sin. Sai dai, bisa dukkan alamu kamar yadda aka yi hasashe, ita ce ta fi jin radadin matakan a jikinta. Misali, a cewar sakatariya Gina Raimondo, idan Sin ta koma matakin da take a shekarar 2019 a bangaren yawo bude ido kadai, to hakan zai karawa Amurkar dala biliyan 30 cikin tattalin arzikinta tare da samar da guraben ayyukan yi sama da 50,000.

  • Daga watan Janairu zuwa Yuli, kudaden shigar kasuwancin software na kasar Sin ya karu da 13.6%

Da alamu irin dimbin alfanun da kasar Sin za ta kawo mata ne ya sa take son kyautata hulda tsakaninta da Sin musamman ta fuskar cinikayya, ganin yadda ta soke jerin sunayen wasu kamfanonin Sin da a baya ta sanyawa takunkumai, gabanin ziyarar madam Raimondo.

Cikin lokaci mai tsawo, kasar Sin ta jajirce wajen raya kanta tare da zama mai matukar muhimmanci ta fuskar samar da kayayyaki da cinikayya da ma jagorantar bangarorin kere-kere daban-daban, lamarin da ya sanya ta zama wani bangare mai matukar muhimmanci ga kamfanonin kasashen waje, ciki har da na Amurka.

A ganina, yadda kasar Sin ke ci gaba da samun habakar tattalin arziki, da kuma yadda Amurka ke jin radadin illolin matakanta, sun tilastawa Amurka neman kyautata huldarta da kasar Sin, bisa la’akari da yadda jami’anta ke ci gaba da kawo ziyara kasar.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Kamar yadda bangarorin biyu suka bayyana, za su kyautata tuntubar juna a tsakaninsu domin a rika tattaunawa a kai a kai. Ko shakka babu, rashin fahimta na daya daga cikin matsalolin da a kan samu a dangantakar manyan kasashen biyu. Don haka, tuntubar juna zai taka muhimmiyar rawa wajen fahimtar manufofi da dabarun juna.

Duk da cewa Amurka na nuna kudurinta na son kyautata hulda tsakaninta da kasar Sin, ta kan kuma aiwatar da abubuwan da su kan saba da huldar kasa da kasa. Amurka ta fi mayar da hankali ne kan ribar da za ta samu ko da kuwa daya bangaren zai yi asara, yayin da kasar Sin ke neman moriyar juna domin a gudu tare a tsira tare. Shawara dai ya ragewa Amurka, ko ta cika alkawuran da ta dauka da girmama alakarta da Sin, ko ta ci gaba da dandana kudarta. (Faeza Mustapha)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS Ta Bude Ofishin Samar Da Ingantaccen Fasfo A Zariya

Next Post

Babu Kasar Da Za Ta Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tabbatuwar Tsaro Ba

Related

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

3 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

4 hours ago
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

4 hours ago
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

5 hours ago
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

7 hours ago
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

9 hours ago
Next Post
Babu Kasar Da Za Ta Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tabbatuwar Tsaro Ba

Babu Kasar Da Za Ta Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tabbatuwar Tsaro Ba

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.