ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Amurka Za Ta Cika Alkawurranta A Wannan Karon?

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

Ziyarar sakatariyar harkokin cinikayya na Amurka Gina Raimondo a kasar Sin, tana ci gaba da daukar hankalin kafafen yada labarai, inda ake bayyana mabambantan ra’ayoyi.

Tuni dai muka riga mu kan san cewa, Amurka ce ta fara kaddamarwa tare da ci gaba da rura yakin cinikayya tsakaninta da Sin. Sai dai, bisa dukkan alamu kamar yadda aka yi hasashe, ita ce ta fi jin radadin matakan a jikinta. Misali, a cewar sakatariya Gina Raimondo, idan Sin ta koma matakin da take a shekarar 2019 a bangaren yawo bude ido kadai, to hakan zai karawa Amurkar dala biliyan 30 cikin tattalin arzikinta tare da samar da guraben ayyukan yi sama da 50,000.

  • Daga watan Janairu zuwa Yuli, kudaden shigar kasuwancin software na kasar Sin ya karu da 13.6%

Da alamu irin dimbin alfanun da kasar Sin za ta kawo mata ne ya sa take son kyautata hulda tsakaninta da Sin musamman ta fuskar cinikayya, ganin yadda ta soke jerin sunayen wasu kamfanonin Sin da a baya ta sanyawa takunkumai, gabanin ziyarar madam Raimondo.

ADVERTISEMENT

Cikin lokaci mai tsawo, kasar Sin ta jajirce wajen raya kanta tare da zama mai matukar muhimmanci ta fuskar samar da kayayyaki da cinikayya da ma jagorantar bangarorin kere-kere daban-daban, lamarin da ya sanya ta zama wani bangare mai matukar muhimmanci ga kamfanonin kasashen waje, ciki har da na Amurka.

A ganina, yadda kasar Sin ke ci gaba da samun habakar tattalin arziki, da kuma yadda Amurka ke jin radadin illolin matakanta, sun tilastawa Amurka neman kyautata huldarta da kasar Sin, bisa la’akari da yadda jami’anta ke ci gaba da kawo ziyara kasar.

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Kamar yadda bangarorin biyu suka bayyana, za su kyautata tuntubar juna a tsakaninsu domin a rika tattaunawa a kai a kai. Ko shakka babu, rashin fahimta na daya daga cikin matsalolin da a kan samu a dangantakar manyan kasashen biyu. Don haka, tuntubar juna zai taka muhimmiyar rawa wajen fahimtar manufofi da dabarun juna.

Duk da cewa Amurka na nuna kudurinta na son kyautata hulda tsakaninta da kasar Sin, ta kan kuma aiwatar da abubuwan da su kan saba da huldar kasa da kasa. Amurka ta fi mayar da hankali ne kan ribar da za ta samu ko da kuwa daya bangaren zai yi asara, yayin da kasar Sin ke neman moriyar juna domin a gudu tare a tsira tare. Shawara dai ya ragewa Amurka, ko ta cika alkawuran da ta dauka da girmama alakarta da Sin, ko ta ci gaba da dandana kudarta. (Faeza Mustapha)

 

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Next Post
Babu Kasar Da Za Ta Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tabbatuwar Tsaro Ba

Babu Kasar Da Za Ta Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tabbatuwar Tsaro Ba

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.