• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Audu Maikaba Zai Iya Kawo Gyara A Kano Pillars?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Me Ya Sa Kano Pillars Ta Fada Ajin Gajiyayyu A Nijeriya?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin wannan satin ne shugabancin kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ya tabbatar da Abdullahi Maikaba a matsayin sabon kocin kungiyar bayan daukar tsawon lokaci ana tattaunawa da masu koyarwa da dama da suka nuna sha’awar koyar da kungiyar.

Maikaba ya rattaba hannu kan kwangilar shekara biyu da kungiyar da ake kira ”SAI MASU GIDA” daga kakar wasa ta 2023 zuwa 2024 zuwa 2024/2025, kuma zai yi aiki tare da Abubakar Abubakar da ake kira Senior da Ahmad Garba Yaro Yaro da Gambo Muhammad sai kuma Auwalu Abbas a matsayin mai horar da masu tsaron gida.

  • Shin Kano Pillars Za Ta Dawo Hayyacinta?

Da yake kaddamar da kocin a ofishinsa, mataimakin gwamnan jihar Kano, Kwamared Aminu AbdulSalam Gwarzo, ya bukace shi da ya zage dantse domin farfado da martabar kungiyar.

Mataimakin gwamnan, ya taya shi murna tare da bayyana nadin nasa a matsayin wanda ya dace ganin irin dumbin kwarewarsa a harkar koyar da kwallon kafa a kungiyoyin daban-daban a Nijeriya.

Mataimakin Gwamnan ya yi alkawarin ci gaba da bai wa kungiyar goyon baya domin ganin an cimma burin da aka sanya a gaba, sannan kuma ya bayar da tabbacin cewa nan ba da jimawa ba gwamnatin Kano za ta kara kaimi wajen gyaran filin wasa na Sani Abacha da ke kofar mata Kano.

Labarai Masu Nasaba

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Ya yaba wa shugabannin kungiyar da ‘yan wasan kungiyar bisa kwazon da suka nuna wanda ya sa kungiyar ta koma gasar Premier ta kasa duba da irin tarihin da kungiyar take da shi a gasar.

Da yake mayar da martani, Abdullahi Maikaba ya gode wa mahukuntan kungiyar da suka amince da shi sannan ya yi alkawarin tabbatar da amincewar da aka yi masa domin koyar da kungiyar.

Idan mai karatu bai manta ba a bara ne Kano Pillars ta fadi daga gasar Firimiya ta kasa, wadda ta koma buga gasa mai daraja ta biyu, wadda za ta buga babbar gasa ta bana a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Burin Sheikh Dahiru Bauchi Daya Tak Da Ya Rage Masa -Sayyadi Aliyu

Next Post

Zulum Ya Cire Sunan Ngoshe Daga Sunayen Kwamishinonin Borno

Related

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu
Wasanni

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

3 hours ago
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan
Wasanni

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

5 hours ago
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal
Wasanni

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

6 hours ago
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona
Wasanni

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

2 days ago
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Wasanni

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

4 days ago
Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala ÆŠaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

5 days ago
Next Post
Zulum Ya Cire Sunan Ngoshe Daga Sunayen Kwamishinonin Borno

Zulum Ya Cire Sunan Ngoshe Daga Sunayen Kwamishinonin Borno

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Kano Pillars

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.