• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Ko Liverpool Za Ta Iya Kai Bantenta A Bana Kuwa?

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Liverpool

Liverpool

Kungiyar kwallon kafa ta Liberpool tana fuskantar kakar wasa mai wahala cikin shekaru sama da bakwai, sakamakon rashin nasarar da kungiyar ta yi a hannun kungiyar kwallon kafa ta Leeds United a satin da ya gabata.

Kawo yanzu dai, Liberpool tana mataki na tara a kan teburin gasar Premier League da maki 16, bayan buga wasanni 12 a gasar Ingila ta bana, kuma yanzu Liberpool ta ci wasanni hudu da canjaras hudu aka doke ta a karawa hudu, bayan da wasa biyu ta yi rashin nasara a bara da ta yi ta biyu a gasar.

  • Tsegunta Barazanar Tsaro Daga Ofishin Jakadancin Amurka: Wa Abin Zai Amfanar?
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Samar Da Fa’ida A Zahiri Ga Jama’ar Afirka

A ranar Asabar Leeds United ta doke Liberpool da ci 2-1 a filin wasa na Anfield a wasan mako na 14 a Premier League, kuma karon farko da aka ci kungiyar a filin wasanta na Anfield tun bayan wasa 29 a jere ba a doke ta ba, rabon da ta yi rashin nasara tun 1-0 da Fulham ta yi a Maris din shekara ta 2021.

Cikin wasanni 29 da ta buga a Anfield ba tare da rashin nasara ba a jere ta ci 22 da yin canjaras bakwai. Liberpool ta yi rashin nasara a wasa biyu a jere kenan, bayan da tun farko Nottingham Forest ta yi nasara da ci 1-0.

Rashin nasara da Liberpool ta yi a Anfield shi ne karon farko tare da mai tsaron baya Birgil ban Dijk a cikin fili, wanda ya yi wasanni 70 a gida ba a doke kungiyar ba, sannan Liberpool za ta buga wasa daya a Premier League kafin a je gasar kofin duniya, shi ne wanda za ta karbi bakuncin Southampton ranar 12 ga watan Nuwamba.

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Sai dai lokacin da Liberpool za ta dan sarara har sai bayan gasar kofin duniya, watakila ta kamo bakin zaren, amma kuma me ya sa Liberpool ba ta kokari a bana duk da cefanen da ta yi bayan da ta kare a mataki na biyu a bara da Manchester City ta lashe kofin?

Tun a farko, wasu na cewa duk inda Jurgen Kloop ya yi shekara bakwai a kungiya ya kan ci karo da kalubale a shekara ta takwas, saboda wasu na cewa salon wasa iri daya yake yi shi ya sa idan ya yi shekara bakwai kowa ke gane dabararsa a fagen horar da kwallo.

Haka ya faru a Mainz da Borussia Dortmund da ya yi kaka bakwai a kowacce kungiyar, amma ya kasa kai bantensa a shekara ta takwas kuma ana ganin cewa yawan rauni da ‘yan wasan Liberpool ke yi na daya daga cikin abin da ya sa kungiyar ke fuskantar koma-baya.

‘Yan wasan kungiyar da ke jiyya kawo yanzu sun hada da Thiago Alcantara da Luis Diaz da Diogo Jota da Ibrahima Konate da Joel Matip da Arthur Melo kuma dukkaninsu suna daya daga cikin ‘yan wasan da ke taimaka wa kungiyar.

Sannan a wannan kakar dan wasa Mohamed Salah baya cin kwallo kamar yadda ya kamata, domin kafin wasa da Leeds United kwallo uku ya zura a raga mafi karanci, wanda a Oktoban ya kan ci biyar.

Haka kuma ana hasashen cewar wasu ‘yan kwallon Liberpool shekarunsu sun ja, ya kamata ta kara daukar wasu masu jini a jika ta kara sirkawa idan har tana son ta ci gaba da jan zarenta irin na baya.

Sannan wasu suna ganin tafiyar dan wasa Sadio Mane zuwa kungiyar Bayern Munich a bana ya taba Liberpool, wadda ta dauko Darwin Nunez, wanda ya maye gurbin dan kwallon tawagar Senegal din.

Nunez ya ci kwallo hudu a Premier League ta bana an kuma yi masa jan kati a kakar bana, to sai dai kuma Liberpool na kokari a Champions League, bayan da ta samu gurbin shiga wasannin gaba na kungiyoyi 16.

A ranar Lahadin da ta gabata, Liberpool za ta fafata da kungiyar kwallon kafa ta Tottenham a gasar firimiya, wasan da kungiyar take bukatar lashewa idan har tana fatan ganin ta ci gaba da neman kammala gasar ta Firimiya a mataki na hudun farko.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0
Wasanni

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane
Wasanni

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni
Wasanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Next Post
EFCC Ta Ƙwace Gidaje 40 Da Wasu Wurare Mallakar Sanata Ekweremedu

EFCC Ta Ƙwace Gidaje 40 Da Wasu Wurare Mallakar Sanata Ekweremedu

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.