• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Manchester City Za Ta Kai Bantenta Babu Rodri?

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
12 months ago
in Wasanni
0
Shin Manchester City Za Ta Kai Bantenta Babu Rodri?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan wasa Rodri za a iya cewa shi ne jigon nasarar kungiyar kwallon kafa ta Manchester City, a ‘yan shekarun nan tun bayan komawarsa kasar Ingila da buga wasa daga kungiyar kwallon kafa ta Atletico Madrid ta kasar Spaniya.

 

Dan wasan na Manchester City, ya ji rauni ranar Lahadi a karawar da suka tashi 2-2 da Arsenal a Premier League duk da cewa har yanzu ba a fayyace girman raunin ba, balle a tabbatar da kwanakin da zai yi jinya da ranar da zai koma fili, amma wasu na cewar zai dauki lokaci mai tsawo.

  • Gundogan Ya Amince Ya Sake Komawa Manchester City 
  • Babban Taron Samar Da Kayayyaki Na 2024 Ya Sa Kaimi Ga Kulla Ayyukan Hadin Gwiwa 718

Sai dai Pep Guardiola, kociyan kungiyar ta Manchester City, bai taba boyewa ba cewar da wuya a samu wanda zai maye gurbin Rodri a kungiyar daga gurbin masu buga tsakiya wanda hakan ya sa kungiyar za ta shiga halin tsaka mai wuya. Dan wasa Kalbin Philips ana ganin zai iya buga gurbin Rodri, to amma Guardiola na hangen yana da sauran gogewa, shi ya sa ya bayar da aronsa ga kungiyar kwallon kafa ta Ipswich kuma yarjejeniya ce ta kakar wasa daya.

 

Labarai Masu Nasaba

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Wasu na ganin watakila Guardiola ya sauya tsarin yadda zai ke fara wasa ta yadda zai ke samun sauki wajen fuskantar kungiyoyi ba tare da an yi masa illa ba kuma tsohon dan wasan Chelsea, Matea Kobacic zai iya buga gurbin Rodri, ba shi kadai ne zabi ba a kungiyar ba.

 

John Stone kan buga tsakiya amma ba ya hawa sama sosai, domin yana aikin mai tsaron baya ne, wasu lokutan yana yi daga gefen hagu, kenan ana iya saka shi a gurbin mai wasa daga tsakiya sai Ilkay Gundogan shi ma ya buga gurbin da Rodri ke yi tun kafin ya bar Manchester City zuwa Barcelona a shekarar 2023, wanda yanzu ya sake komawa City din a bana.

 

Haka kuma Manchester City tana amfani da Bernardo Silba ga kuma Kebin de Bruyne, wanda ke jinya, sannan akwai matashi mai shekara 19, Rico Lewis wanda Guardiola ya ce zabi ne a wajensa, wanda ya kware a buga gurbi da yawa.

 

Idan har Rodri ya dade yana jinya, hakika zai kawo koma baya a Manchester City a bana, amma dai Guardiola ya kwan da sanin ya zama wajibi ya dauki mataki tun kafin dare ya yi masa, har ila yau an rufe kasuwar sayar da ‘yan wasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArsenalManchesterUEFA Champions League
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda, Sun Kama Ɓarayin Shanu 22

Next Post

Manyan Batutuwan Taron Sanatoci Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya A Kano

Related

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica
Wasanni

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

3 hours ago
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff
Wasanni

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

4 days ago
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana
Wasanni

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

4 days ago
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa
Wasanni

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

4 days ago
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?
Wasanni

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

4 days ago
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
Wasanni

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

6 days ago
Next Post
Manyan Batutuwan Taron Sanatoci Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya A Kano

Manyan Batutuwan Taron Sanatoci Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya A Kano

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.