• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Manchester City Za Ta Kai Bantenta Babu Rodri?

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
8 months ago
in Wasanni
0
Shin Manchester City Za Ta Kai Bantenta Babu Rodri?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan wasa Rodri za a iya cewa shi ne jigon nasarar kungiyar kwallon kafa ta Manchester City, a ‘yan shekarun nan tun bayan komawarsa kasar Ingila da buga wasa daga kungiyar kwallon kafa ta Atletico Madrid ta kasar Spaniya.

 

Dan wasan na Manchester City, ya ji rauni ranar Lahadi a karawar da suka tashi 2-2 da Arsenal a Premier League duk da cewa har yanzu ba a fayyace girman raunin ba, balle a tabbatar da kwanakin da zai yi jinya da ranar da zai koma fili, amma wasu na cewar zai dauki lokaci mai tsawo.

  • Gundogan Ya Amince Ya Sake Komawa Manchester City 
  • Babban Taron Samar Da Kayayyaki Na 2024 Ya Sa Kaimi Ga Kulla Ayyukan Hadin Gwiwa 718

Sai dai Pep Guardiola, kociyan kungiyar ta Manchester City, bai taba boyewa ba cewar da wuya a samu wanda zai maye gurbin Rodri a kungiyar daga gurbin masu buga tsakiya wanda hakan ya sa kungiyar za ta shiga halin tsaka mai wuya. Dan wasa Kalbin Philips ana ganin zai iya buga gurbin Rodri, to amma Guardiola na hangen yana da sauran gogewa, shi ya sa ya bayar da aronsa ga kungiyar kwallon kafa ta Ipswich kuma yarjejeniya ce ta kakar wasa daya.

 

Labarai Masu Nasaba

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Wasu na ganin watakila Guardiola ya sauya tsarin yadda zai ke fara wasa ta yadda zai ke samun sauki wajen fuskantar kungiyoyi ba tare da an yi masa illa ba kuma tsohon dan wasan Chelsea, Matea Kobacic zai iya buga gurbin Rodri, ba shi kadai ne zabi ba a kungiyar ba.

 

John Stone kan buga tsakiya amma ba ya hawa sama sosai, domin yana aikin mai tsaron baya ne, wasu lokutan yana yi daga gefen hagu, kenan ana iya saka shi a gurbin mai wasa daga tsakiya sai Ilkay Gundogan shi ma ya buga gurbin da Rodri ke yi tun kafin ya bar Manchester City zuwa Barcelona a shekarar 2023, wanda yanzu ya sake komawa City din a bana.

 

Haka kuma Manchester City tana amfani da Bernardo Silba ga kuma Kebin de Bruyne, wanda ke jinya, sannan akwai matashi mai shekara 19, Rico Lewis wanda Guardiola ya ce zabi ne a wajensa, wanda ya kware a buga gurbi da yawa.

 

Idan har Rodri ya dade yana jinya, hakika zai kawo koma baya a Manchester City a bana, amma dai Guardiola ya kwan da sanin ya zama wajibi ya dauki mataki tun kafin dare ya yi masa, har ila yau an rufe kasuwar sayar da ‘yan wasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArsenalManchesterUEFA Champions League
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda, Sun Kama Ɓarayin Shanu 22

Next Post

Manyan Batutuwan Taron Sanatoci Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya A Kano

Related

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

3 days ago
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 
Wasanni

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

3 days ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

6 days ago
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro
Wasanni

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

6 days ago
PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 
Wasanni

PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 

7 days ago
UEFA: Inter Milan Ta Yi Wa Barcelona Kancal
Wasanni

UEFA: An Kai Ruwa Rana Yayin Da Inter Ta Koro Barcelona Gida

1 week ago
Next Post
Manyan Batutuwan Taron Sanatoci Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya A Kano

Manyan Batutuwan Taron Sanatoci Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya A Kano

LABARAI MASU NASABA

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.