ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Batutuwan Taron Sanatoci Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya A Kano

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Kano

Kwamitin Majalisar Dattijai na gyaran kundin tsarin mulkin 1999 ya fara wani taron tattaunawar kwanaki biyu a Kano, tare da nufin kammala aikin gyaran kundin tsarin mulki kafin watan Disamba 2025.

Taron, wanda aka shirya tare da haɗin gwuiwar Cibiyar Tsarin Dokoki da Inganta Siyasa (PLAC), na da nufin magance batutuwan da suka haɗa da ƴancin ƙananan hukumomi, da kafa ƴansandan jihohi, da kuma bai wa Sarakunan gargajiya dama a gwamnatance domin magance matsalar tsaro.

  • Sanata Barau Jibrin Ya Ƙaddamar Da Motocin Zirga-Zirga A Kano
  • Jihar Kano Ta Musanta Zargin Karɓar Bashin Biliyan 177 Daga Faransa

Masu jawabi, ciki har da Sanata Jibrin Barau, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattijai, sun jaddada mahimmancin haɗin kai da masu ruwa da tsaki kamar gwamnoni, da majalisun jihohi, da ɓangaren shari’a, da ƙungiyoyin farar hula domin tabbatar da samun nasarar wannan gyara.

ADVERTISEMENT

Barau ya yi kira da a samar da hadin kai tsakanin dukkan ɓangarorin majalisar dokoki guda biyu sannan ya buƙaci a yi la’akari sosai da shawarwarin da za su kawo canji mai ɗorewa ga al’ummar Nijeriya.

Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu, ya jaddada mahimmancin ɗaukar mataki cikin lokaci da kuma tsara ayyuka yadda ya dace domin kaucewa karkatar da hankalin jama’a yayin da zaɓe ke gabatowa.

LABARAI MASU NASABA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

Kwamitocin majalisar dattijai da na wakilai sun shirya gudanar da tarukan sauraron ra’ayoyin jama’a tare da Sarakunan gargajiya da shugabannin siyasa domin samun cikakken bayani.

Sauran masu jawabi, ciki har da Hon. Adebo Edward Ogundoyin, Shugaban Taron Shugabannin Majalisun Jihohi, da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan, sun buƙaci a mayar da hankali kan ƴancin mata, da ƴancin ƙananan hukumomi, da kuma rawar da Sarakuna zasu iya takawa a hukumance.

Kano
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Ɗiyata Tilo Ta Mutu A Wata Makarantar Sakandire A Kano – Mahaifiya
  • Abubakar Sulaiman
    INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6
  • Abubakar Sulaiman
    Shigo Da Fetur Ya Ƙaru Da Kashi 59.5% A Watan Mayu A Nijeriya — NMDPRA

MASU ALAKA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

June 19, 2026
INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6
Manyan Labarai

INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6

June 19, 2026
Next Post
Gwamatin Amurka Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Mata ‘Yan Kasuwa A Nijeriya

Gwamatin Amurka Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Mata ‘Yan Kasuwa A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

June 20, 2026
2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.