• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin ziyarar da Nancy Pelosi ke shirin kai wa Taiwan ba Takala ba ce?

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shin ziyarar da Nancy Pelosi ke shirin kai wa Taiwan ba Takala ba ce?

Speaker of the House Nancy Pelosi, D-Calif., reacts to the Supreme Court decision overturning Roe v. Wade, at the Capitol in Washington, Friday, June 24, 2022. (AP Photo/J. Scott Applewhite)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ko shakka babu, burin Amurka shi ne tada hankalin duniya domin cimma wani muradi nata na kashin kai. Kuma dukkan alamu sun nuna cewa, sam ba ta kaunar zaman lafiya.

A ranar Juma’ar da ta gabata, shugaban Amurka ya bayyana cewa, kasarsa na girmama manufar kasar Sin daya tak a duniya, kuma ba ta goyon bayan ’yancin kan yankin Taiwan.

Sai dai har kullum, Amurkar kan yi amai ne ta lashe. Yayin da shugaban kasar ya bayyana haka tare da cewa hadin gwiwar Sin da kasarsa na da muhimmanci ga zaman lafiyar duniya, sai kuma aka ji shugabar majalisar wakilan kasar Nancy Pelosi na shirin ziyartar yankin na Taiwan.

Wannan fa na zuwa ne bayan kasar Sin ta yi gargadi da babbar murya game da hakan. Har kullum, shugaban Amurka kan furta wani abu dake karfafa gwiwar alakar kasarsa da Sin za ta kyautata domin amfanin al’ummun duniya, amma kuma, sai ’yan siyasar kasar su furta ko aiwatar da wani abu da ya sabawa hakan. Shin babu fahimta ne tsakanin shugaban kasar Amurka da sauran ’yan siyasar kasar? Ko kuma wani salo ne na makircin Amurka?

Idan Amurkar ba ta sani ba, wannan yana kara zubar da kimarta ne a idon duniya. Domin a ranar Juma’a, duk da muhimman batutuwa da aka tabo, an yi tsammanin ganin kyautatuwar lamura da dangantaka tsakanin manyan kasashen biyu, amma kuma batun ziyarar Nancy Pelosi, ya kawar da wannan tunani.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

Duk inda Amurka ta shiga, ta tsoma baki cikin harkokinsu na gida, to ba a karewa lafiya. Ga misali nan na zahiri ana gani a kan Ukraine, lamarin da ba kasashen dake rikicin kawai ya shafa ba, har da na shiyyarsu da sauran nahiyoyi, kai da daukacin duniya.

Kasar Sin dai, ta yi gargadi game da rashin amincewarta da ziyarar ta Nancy Pelosi a yankin Taiwan. Taiwan, yanki ne mallakar kasar Sin, don hak duk wata hulda ta jakadanci ta kai tsaye da yankin, ya keta manufar Sin daya tak a duniya, da tubalin hadin gwiwar Sin da kowacce kasa, haka zalika, ya take dokokin huldar kasa da kasa. Bisa la’akari da hakan, duk wata alaka ta kai tsaye da yankin, abu daya yake nufi, wato takalar fada.

A bayyane yake cewa, burin Amurka shi ne kokarin ta da rikici a Sin, ta daidaita al’ummar kasar sama da biliyan 1.4 dake zaune lami lafiya, da hargitsa tattalin arzikinta da tasiri da ma karfinta a duniya, sannan za ta ja gefe ta bar Taiwan, hakarta ta cimma ruwa ke nan.
A nata bangare dai kasar Sin kamar kowacce kasa mai sanin ya kamata, burinta shi ne tabbatar da dunkulewar kasar cikin lumana, sai dai kuma, hakan ba ya nufin za ta kyale ana yadda aka ga dama da yankunanta. Ta kuma nanata cewa, za ta yi dukkan mai yuwuwa, ciki har da daukar matakan soji, domin kare cikakken ’yanci da iko da yankunanta.(Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Mayar Da Martani Ga Yadda Nancy Pelosi Ta Je Yankin Taiwan Na Kasar

Next Post

Kwamishinan Yobe, Goni Bukar, Ya Rasu A Hadarin Mota

Related

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

54 minutes ago
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

1 hour ago
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

20 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

21 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

23 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

23 hours ago
Next Post
Kwamishinan Yobe, Goni Bukar, Ya Rasu A Hadarin Mota

Kwamishinan Yobe, Goni Bukar, Ya Rasu A Hadarin Mota

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

August 27, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

August 27, 2025
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

August 27, 2025
Nijeriya Za Ta ÆŠaukaka Da Fasahar Ƙere-Æ™ere Da Tattalin Abinci – Tinubu

Nijeriya Za Ta ÆŠaukaka Da Fasahar Ƙere-Æ™ere Da Tattalin Abinci – Tinubu

August 27, 2025
Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.