ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin ziyarar da Nancy Pelosi ke shirin kai wa Taiwan ba Takala ba ce?

by CMG Hausa
4 years ago
Speaker of the House Nancy Pelosi, D-Calif., reacts to the Supreme Court decision overturning Roe v. Wade, at the Capitol in Washington, Friday, June 24, 2022. (AP Photo/J. Scott Applewhite)

Speaker of the House Nancy Pelosi, D-Calif., reacts to the Supreme Court decision overturning Roe v. Wade, at the Capitol in Washington, Friday, June 24, 2022. (AP Photo/J. Scott Applewhite)

Ko shakka babu, burin Amurka shi ne tada hankalin duniya domin cimma wani muradi nata na kashin kai. Kuma dukkan alamu sun nuna cewa, sam ba ta kaunar zaman lafiya.

A ranar Juma’ar da ta gabata, shugaban Amurka ya bayyana cewa, kasarsa na girmama manufar kasar Sin daya tak a duniya, kuma ba ta goyon bayan ’yancin kan yankin Taiwan.

Sai dai har kullum, Amurkar kan yi amai ne ta lashe. Yayin da shugaban kasar ya bayyana haka tare da cewa hadin gwiwar Sin da kasarsa na da muhimmanci ga zaman lafiyar duniya, sai kuma aka ji shugabar majalisar wakilan kasar Nancy Pelosi na shirin ziyartar yankin na Taiwan.

ADVERTISEMENT

Wannan fa na zuwa ne bayan kasar Sin ta yi gargadi da babbar murya game da hakan. Har kullum, shugaban Amurka kan furta wani abu dake karfafa gwiwar alakar kasarsa da Sin za ta kyautata domin amfanin al’ummun duniya, amma kuma, sai ’yan siyasar kasar su furta ko aiwatar da wani abu da ya sabawa hakan. Shin babu fahimta ne tsakanin shugaban kasar Amurka da sauran ’yan siyasar kasar? Ko kuma wani salo ne na makircin Amurka?

Idan Amurkar ba ta sani ba, wannan yana kara zubar da kimarta ne a idon duniya. Domin a ranar Juma’a, duk da muhimman batutuwa da aka tabo, an yi tsammanin ganin kyautatuwar lamura da dangantaka tsakanin manyan kasashen biyu, amma kuma batun ziyarar Nancy Pelosi, ya kawar da wannan tunani.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Duk inda Amurka ta shiga, ta tsoma baki cikin harkokinsu na gida, to ba a karewa lafiya. Ga misali nan na zahiri ana gani a kan Ukraine, lamarin da ba kasashen dake rikicin kawai ya shafa ba, har da na shiyyarsu da sauran nahiyoyi, kai da daukacin duniya.

Kasar Sin dai, ta yi gargadi game da rashin amincewarta da ziyarar ta Nancy Pelosi a yankin Taiwan. Taiwan, yanki ne mallakar kasar Sin, don hak duk wata hulda ta jakadanci ta kai tsaye da yankin, ya keta manufar Sin daya tak a duniya, da tubalin hadin gwiwar Sin da kowacce kasa, haka zalika, ya take dokokin huldar kasa da kasa. Bisa la’akari da hakan, duk wata alaka ta kai tsaye da yankin, abu daya yake nufi, wato takalar fada.

A bayyane yake cewa, burin Amurka shi ne kokarin ta da rikici a Sin, ta daidaita al’ummar kasar sama da biliyan 1.4 dake zaune lami lafiya, da hargitsa tattalin arzikinta da tasiri da ma karfinta a duniya, sannan za ta ja gefe ta bar Taiwan, hakarta ta cimma ruwa ke nan.
A nata bangare dai kasar Sin kamar kowacce kasa mai sanin ya kamata, burinta shi ne tabbatar da dunkulewar kasar cikin lumana, sai dai kuma, hakan ba ya nufin za ta kyale ana yadda aka ga dama da yankunanta. Ta kuma nanata cewa, za ta yi dukkan mai yuwuwa, ciki har da daukar matakan soji, domin kare cikakken ’yanci da iko da yankunanta.(Fa’iza Mustapha)

nancy pelosi
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Kwamishinan Yobe, Goni Bukar, Ya Rasu A Hadarin Mota

Kwamishinan Yobe, Goni Bukar, Ya Rasu A Hadarin Mota

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.