ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin 3MTT Zai Samar Wa Matasa Miliyan Uku Aikin Yi, inji Ministan Yaɗa Labarai

by Sulaiman
1 year ago
Amurka

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa, gwamnatin Tinubu ta shirya tsaf don samar da ayyukan yi miliyan uku ga matasan Nijeriya ta hanyar Shirin 3MTT.

 

Ministan ya bayyana hakan ne a Abuja ranar Litinin a Taron Matasa ‘Yansandan Nijeriya mai taken “Inganta Ƙimar Matasan Nijeriya don Tsaron Ƙasa.”

ADVERTISEMENT
  • Nijeriya Ta Fara Sayar Da Makaman Da Ta Ke Kerawa – Minista
  • Mutum 3 Sun Rasa Rayukansu Yayin Da Ambaliyar Ruwa Ta Mamaye Ƙauyuka A Bauchi

Ministan, wanda ya samu wakilcin Darakta Janar na hukumar gidan rediyon Muryar Nijeriya (VoN), Malam Jibrin Baba Ndace, ya ce shirin na 3MTT, wanda Ma’aikatar Sadarwa ke jagoranta, wani shiri ne na ilimi da ƙwarewar da za su inganta iyawa da ƙimar matasa a harkar tsaron ƙasa.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

Ya ce: “Shirin 3MTT tabbaci ne na burin Shugaba Tinubu na samar da cigaban matasa a cikin dabarun cigaban ƙasa baki ɗaya. Domin samar da kyakkyawan tsari don cimma wannan, gwamnatin tana kuma ba da fifiko ga tattalin arzikin matasan Nijeriya, wajen gina ƙasa mai tsaro da wadata.”

 

Idris ya ce kafa Asusun Ba Da Lamuni na Ilimi na Nijeriya (NELFUND), wanda a halin yanzu yake bayar da lamuni da tallafin kuɗi ga ɗaliban Nijeriya, yana ɗaya daga cikin manyan tsare-tsare a ƙarƙashin Shirin Sabunta Fata na Shugaba Tinubu, da nufin yin tasiri sosai kan neman ilimi na matasa.

 

A yayin da yake magana kan tsadar sufuri a ƙasar nan, ministan ya ce Shugaban Ƙasa ya ɓullo da shirin CNG don amfani da isasshiyar iskar gas da ƙasar ke da ita wajen rage farashin sufuri da kusan kashi 70.

 

Ministan ya kuma jaddada buƙatar da ke akwai ta matasa su yi koyi da kyawawan ɗabi’un da suka dace domin su taka rawar su a harkar tsaron ƙasa.

 

Sai dai ministan ya gargaɗi matasa kan illolin da yaɗa labaran ƙarya ke da shi ga tsaron ƙasa, yana mai cewa wannan muguwar ɗabi’a amfani da ‘yancin faɗin albarkacin baki, wanda gwamnati mai ci yanzu ta amince da shi, ta hanyar da ba ta dace ba ne.

 

Ya ce: “Inda aka ba da yawa, ana sa ran da yawa. Dole ne mu yarda cewa yaɗa labaran ƙarya ya haɗu da babbar barazana ga tsaron ƙasa, wadda ta haɗa da tada hankali, rashin zaman lafiya, laifuffuka na ƙasa da ƙasa, ta’addanci, fashi da makami, tsattsauran ra’ayi, da munanan ayyukan da ake yaɗawa ta hanyar intanet.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

December 22, 2025
Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Next Post
Cinikayyar Sin Da Afirka Ta Bunkasa Bisa Daidaito Tsakanin Janairu Da Yuli

Cinikayyar Sin Da Afirka Ta Bunkasa Bisa Daidaito Tsakanin Janairu Da Yuli

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

December 22, 2025
Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.