• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Cusa Ɗa’a Da Kishin Ƙasa: An Fitar Da Daftarin Yaɗa Kyawawan Ɗabi’un Farfaɗo da Martabar Nijeriya

by Sulaiman
2 years ago
Kishin kasa

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya karɓi daftarin yaɗa kyawawan ɗabi’u da cusa ɗa’a domin farfaɗo da martabar Nijeriya.

Da ya ke karɓar daftarin da aka tsara don cusa ɗa’a a zukatan jama’a, Idris wanda a cikin Disamba ya kafa kwamitin tsara daftarin mai mutum 10, ya ce Shugaba Bola Tinubu ne zai ƙaddamar da shirin a cikin wannan shekarar.

  • Za Mu Dawo Da Martabar PDP A Katsina — Kwamitin Riƙon Ƙwarya
  • Tinubu Zai Kori Ministocin Da Ba Su Da Kwazon Aiki – Hadiza Bala Usman

A jawabinsa yayin karɓar daftarin daga hannun Shugaban Kwamitin, Dakta Auwal Haruna, a ranar Talata a Abuja, ministan ya ce gwamnatin Tinubu ta ƙudiri aniyar zayyana kyawawan ɗabi’un da za a cusa ɗa’a a zukatan jama’a ba tare da la’akari da nuna bambanci ko fifita wata ƙabila ko matsayi ba.

Kakakin Yaɗa Labaran Ministan, Malam Rabi’u Ibrahim, sh ne ya fitar da sanarwar bayanin bayan taron karɓar daftarin a gaban sauran ‘yan kwamitin.

Idris ya ce: “Shi muhimmancin Daftarin Ɗa’a da Kishin Ƙasa gwamnati ce a kan gaba wajen ɗabbaƙa shi.”

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Abin Da Daftarin Ya Ƙunsa:

Ministan ya ce daftarin ya ƙunshi Alƙawurra Bakwai da Nijeriya ta ɗaukar wa ‘yan ƙasar ta, sai kuma wasu Ƙudirori Bakwai da ‘yan Nijeriya ya za su ɗauka wajen kare martabar ƙasar su.

Ya ce daftarin zai tafi tare da yin la’akari da irin ɗimbin yawan matasan da wannan ƙasa ke da shi, waɗanda ke rayuwa duniyar da ƙirƙire-ƙirƙiren fasahar zamani ke da tasiri a duniya.

A kan haka ne ya ce gwamnati ta ƙudiri aniyar tabbatar da cewa matasa za su ja ragamar ƙoƙarin bunƙasa ƙasar nan domin samun dauwamammen cigaba.

Ministan ya yaba wa ƙoƙarin da gwamnatocin baya su ka yi wajen haƙilon neman hanyoyin da za a bi domin magance sakwarkwacewar kyawawan ɗabi’u a zukatan ‘yan Nijeriya, ta hanyar bijiro da shirye-shirye daban-daban a baya, irin su “Nigeria: Good People, Great Nation”, “Change Begin With Me”, da sauran su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Bukatar Samar Da Tsaftatacciyar Adawa A Nijeriya

Bukatar Samar Da Tsaftatacciyar Adawa A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.