ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Cusa Ɗa’a Da Kishin Ƙasa: An Fitar Da Daftarin Yaɗa Kyawawan Ɗabi’un Farfaɗo da Martabar Nijeriya

by Sulaiman
2 years ago
Kishin kasa

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya karɓi daftarin yaɗa kyawawan ɗabi’u da cusa ɗa’a domin farfaɗo da martabar Nijeriya.

Da ya ke karɓar daftarin da aka tsara don cusa ɗa’a a zukatan jama’a, Idris wanda a cikin Disamba ya kafa kwamitin tsara daftarin mai mutum 10, ya ce Shugaba Bola Tinubu ne zai ƙaddamar da shirin a cikin wannan shekarar.

  • Za Mu Dawo Da Martabar PDP A Katsina — Kwamitin Riƙon Ƙwarya
  • Tinubu Zai Kori Ministocin Da Ba Su Da Kwazon Aiki – Hadiza Bala Usman

A jawabinsa yayin karɓar daftarin daga hannun Shugaban Kwamitin, Dakta Auwal Haruna, a ranar Talata a Abuja, ministan ya ce gwamnatin Tinubu ta ƙudiri aniyar zayyana kyawawan ɗabi’un da za a cusa ɗa’a a zukatan jama’a ba tare da la’akari da nuna bambanci ko fifita wata ƙabila ko matsayi ba.

ADVERTISEMENT

Kakakin Yaɗa Labaran Ministan, Malam Rabi’u Ibrahim, sh ne ya fitar da sanarwar bayanin bayan taron karɓar daftarin a gaban sauran ‘yan kwamitin.

Idris ya ce: “Shi muhimmancin Daftarin Ɗa’a da Kishin Ƙasa gwamnati ce a kan gaba wajen ɗabbaƙa shi.”

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

Abin Da Daftarin Ya Ƙunsa:

Ministan ya ce daftarin ya ƙunshi Alƙawurra Bakwai da Nijeriya ta ɗaukar wa ‘yan ƙasar ta, sai kuma wasu Ƙudirori Bakwai da ‘yan Nijeriya ya za su ɗauka wajen kare martabar ƙasar su.

Ya ce daftarin zai tafi tare da yin la’akari da irin ɗimbin yawan matasan da wannan ƙasa ke da shi, waɗanda ke rayuwa duniyar da ƙirƙire-ƙirƙiren fasahar zamani ke da tasiri a duniya.

A kan haka ne ya ce gwamnati ta ƙudiri aniyar tabbatar da cewa matasa za su ja ragamar ƙoƙarin bunƙasa ƙasar nan domin samun dauwamammen cigaba.

Ministan ya yaba wa ƙoƙarin da gwamnatocin baya su ka yi wajen haƙilon neman hanyoyin da za a bi domin magance sakwarkwacewar kyawawan ɗabi’u a zukatan ‘yan Nijeriya, ta hanyar bijiro da shirye-shirye daban-daban a baya, irin su “Nigeria: Good People, Great Nation”, “Change Begin With Me”, da sauran su.

Kishin kasa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki
  • Sulaiman
    Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
Labarai

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Next Post
Bukatar Samar Da Tsaftatacciyar Adawa A Nijeriya

Bukatar Samar Da Tsaftatacciyar Adawa A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026
Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.