• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Fim Kan Cikar Nijeriya Shekaru 25 A Kan Turbar Dimokuradiyya: Tasiri Da Muhimmanci

byRabilu Sanusi Bena and Sulaiman
7 months ago
vector illustration of Nigeria flag and map

vector illustration of Nigeria flag and map

Gwamnatin Tarayya ta bayyana shirin ta na ba da goyon baya ga samar da wani shirin fim mai nuna tarihin shekaru 25 na dimokuradiyyar Nijeriya, bayanin hakan ya fito ne daga bakin Ministan Yada Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, a lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin Majalisar Tuntuba ta Jam’iyyun Siyasa, wato Inter-Party Adbisory Council (IPAC), a ranar Juma’ar da ta gabata a Abuja.

Ministan ya bayyana fim din, wanda IPAC ce ta yi tunanin a shirya shi, a matsayin muhimmin tarihin tafiyar da dimokiradiyyar Nijeriya yayin da kasar ke cika shekaru 25 a kan turbar mulkin na mutane, domin mutane kuma daga mutane.

  • Trump Ya Bayyana Dalilin Rufe Gidan Rediyon Muryar Amurka
  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho

Alhaji Muhammad Idris ya ce fim din tarihin zai nuna nasara, kalubale, da darussan da aka koya a wannan tafiya, ya ce “Na yi farin cikin ganin kokarin da IPAC da shugabanninta suke yi wajen karfafa dimokiradiyya, musamman ta hanyar fim din wanda zai zama wata muhimmiyar shaida ta tarihi, domin girmama jajirtattun yan siyasar kasarmu da kuma nuna jajircewar Nijeriya a harkar dimokiradiyya.

A kan haka, Gwamnatin Tarayya, ta hannun Ma’aikatar Yada Labarai da Wayar da Kai, za ta goyi bayan shirya wannan fim na musamman, ya kuma jinjina wa IPAC kan jajircewar ta wajen ci gaban dimokiradiyyar Nijeriya tare da jaddada muhimmancin hadin kan jam’iyyun siyasa bayan zabe domin karfafa hadin kan kasa da kawo ci gaba.

Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu tana goyon bayan a yi gasa mai kyau a siyasa, domin dimokiradiyya ta na bunkasa ne kawai idan ana samun hamayya mai ma’ana da hadin kai bisa muradin kasa ba tare da la’akari da bambancin jam’iyyun siyasa ba,” in ji Idris.

LABARAI MASU NASABA

Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

Ya kuma kara da cewa dorewar tsarin dimokiradiyya na bukatar hadin gwiwa daga kowane bangare, “Jam’iyyun siyasa su ne ginshikin dorewar dimokiraɗiyya, kuma yayin da hamayya take da muhimmanci a lokacin zabe, dole ne mu hada kai wajen gina kasar mu, hakan ya sa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, wanda babban jami’in dimokiradiyya ne yake mutunta gasa mai tsafta, amma kuma ya na fifita hadin kai da ci gaban kasa fiye da komai.

Shugaban IPAC na kasa, Honourable Yusuf Dantalle, ya ce shirin fim din na tarihi zai bayyana ci gaban da aka samu a fannonin gina ababen more rayuwa, kiwon lafiya, ilimi, da hadin kan al’umma, ya kuma ci gaba da “Fim din zai zama wani muhimmin tarihin kasa, zai kuma mayar da hankali kan matasa, musamman ‘yan zamani (Gen Z), domin ya zama wata hanyar ilmantarwa da hade kan ‘yan kasa domin su kara sanin abinda ake nufi da Dimokuradiyya a Nijeriya.

Fim din zai kunshi fitattun jaruman Nollywood kuma za a shirya shi da na’urori na zamani domin ya dace da matakin inganci na duniya, ta yadda babu wani wanda zai kalla ba tare da ya yaba wa wadanda su ka dauki nauyin shirya wannan kasaitaccen shiri.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci
Nazari

Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

September 11, 2025
Mataimakin shugaban kasa
Nazari

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025
haraji
Nazari

Masana Sun Bayyana Yadda Yakin Neman Zaben 2027 Ke Barazana Ga Harkokin Tafiyar Da Gwamnati

May 3, 2025
Next Post
Masarautar Bauchi Ta Sauya Shawara: Za A Yi Hawan Daushe

Masarautar Bauchi Ta Sauya Shawara: Za A Yi Hawan Daushe

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version