• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

by Sani Anwar
3 months ago
in Labarai
0
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai bai wa shugaban kasa shawara, kuma shugaban kwamitin aiwatar da garambawul kan harkokin kiwon dabbobi, Farfesa Attahiru Jega, ya yi gargadin cewa; Nijeriya na iya fuskantar kasadar karancin abinci mai gina jiki ga yara, idan har ba a aiwatar da tsarin sake fasalin kiwon dabbobi na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba.

Ya kuma bayyana cewa, a kokarin da ake yi na cike gibin da ake da shi a bangaren abinci mai gina jiki, Nijeriya na kashe makudan kudade da suka tasamma Naira biliyan 1.5 a duk shekara, wajen shigo da kayayyakin kiwo; wanda galibi madara ta fi yawa, wadda ke da kuma karancin sinadarin gina jiki.

  • APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?
  • Lardin Hainan Na Kasar Sin Ya Samu Karuwar Cinikayyar Hajoji Da Aka Daukewa Haraji Cikin Shekaru Biyar

Haka zalika, Jega ya ce; “Daga nan zuwa shekarar 2030, idan ya kasance an aiwatar da tsare-tsare da kuma gyare-gyare a kan kiwon dabbobi na shirin Shugaba Tinubu, Nijeriya za ta samu nasarar kirkiro ayyukan yi kusan kimanin miliyan biyar ga matasa, ta fuskar samar da wadataccen nama, kiwo, fata da sauran kayayyakin da kamfanoni ke bukata, musamman don taimaka wa matasa da mata a yankunan karkara da birane, wajen samun ayyukan yi.”

Wannan dai na zuwa ne, daidai lokacin da shugaban kwamitin majalisar dattawa mai kula da ayyukan noma da raya karkara, Saliu Mustapha, ya ba da shawarar ware kashi 6 cikin 7 na kasafin kudin Nijeriya, domin samar da ayyukan yi a kasar.

An gudanar da laccar wannan shekara ta 2025 ne kamar yadda aka saba yi a kowace shekara, ranar Litinin da ta gabata a Jami’ar Ilorin da ke Jihar Kwara, don girmama wani dan majalisa.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Taken laccar ita ce, “Tsarin Tattalin Arziki Kan Kiwon Dabbobi A Nijeriya: Kalubale da Nasarori.”

Jega a cikin takardarsa, ya bayyana cewa; “Hasashen da aka yi, ya nuna cewa; nan da shekara ta 2050, al’ummar Nijeriya za ta karu da kusan mutum miliyan 400, wanda hakan zai sanya ta zama kasa ta uku mafi yawan al’umma a duniya. Wannan karuwar yawan jama’a, zai tilasta sake habaka bukatar naman kaji da kashi 253 cikin 100, naman saniya da kashi 117 cikin 100, sai kuma madara da kashi 577 cikin 100, domin biyan bukatun gida.

“Wadannan alkaluma, ba zato ba ne; abubuwa ne da ke kan hanya. Don haka, idan ba a yi kyakkyawan shiri da kuma zuba jari na dogon lokaci a tsarin kiwon dabbobi ba, Nijeriya na iya fuskantar matsalar karancin nama, madara, kara karancin abinci da kuma matsananciyar rayuwa, musamman a yankunan karkara,” in ji Jega.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dabobbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Tuhumar Tsohon Ɗan Wasan Arsenal Thomas Partey Da Laifin Fyaɗe A Ƙasar Ingila

Next Post

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

42 minutes ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

2 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

4 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

7 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

9 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

10 hours ago
Next Post
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.