• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Tinubu Na Samar Da Tabarau Miliyan Biyar Ga Masu Fama Da Ciwon Ido

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Ciwon Ido

LABARAI MASU NASABA

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Ranar Juma’a ta makon da ya gabata ne a Abuja Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da tsarin tallafa wa masu fama da matsalar ido, wanda hadin gwiwa ne tsakanin ma’aikatar lafiya ta tarayya da shirin tsarin lafiyar idanu ta kasa, wato gidauniyar, ‘Peek Bision’ wajen samar wa ‘yan Nijeriya fiye da miliyan biyar da suke fama da matsalar rashin gani sosai Tabarau wanda za su rika amfani da shi.

Shugaban ya tuna da yadda a karo na farko ya taba taimakawa na kusa da shi kan al’amarin da ya shafi lafiyar idanu, wannan ya say a dauki alkawari a madadin gwamnatin tarayya lokacin da aka kai ma shi ziyarar ban girma da jagora kuma shugaban gidauniyar ‘Peek Bision’, har ila yau tare da shi aka kafa gidauniyar  kulawa ta gani,Andrew Bastawrous.

  • Ma’aikatan Kiwon Lafiya 83 Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Cikin Shekara 8 – MHWUN
  • Hukumomin Sin Sun Fitar Da Wasu Ka’idoji Don Inganta Tsaron Wuraren Hakar Ma’adinai

Ya ce “Abu na farko shi ne dangane da wannan al’amari shi ne mahaifiyata Allah ya jikanta, bata lafiyar idanu hakan ne yasa bata iya gane ko wanene ni, amma dana samar mata da taimako aka kula da ita wajen ba da magani da bata Tabarau. Tambayar da ta yi mani ita ce kai nawa ne kai mani wannan abin alhairi, yanzu ya za ayi da mata da yara wadanda basu da wadanda za su  taimaka masu?.

“Sai na yi mata alkawarin zan taimaka wa mutane da yawa ta hanyar kulawa da lafiyar idanunsu ba da wasa ba, shi taimakon kulawa da lafiyar ido kyauta ne tare da yin gwaji da kuma tiyata, saboda tambayar da mahaifiyata ta yi mani da sha’awarta ta a taimakawa wajen raba wasu da cutar.

Daga karshe mun taimaka wa lafiyar idanun miliyoyin mutane a Legas za kuma za a iya lura da hakan wajen farin ciki da annashuwar da su ke ciki, domin an kara inganta masu al’amarin ganinsu ta hanyar basu Tabarau, kamar yadda Shugaban yace.

Da yake kara jaddada muhimmancin kulawa da inganta kulawa da lafiyar idanu a Nijeriya Shugaban kasa Tinubu ya nuna damuwarsa inda ya ce fiye da mutane milyan 24 suna fama da matsalolin da suka shafi idanu daban-daban.

“Lokaci ya yi wanda za mu dauki mataki saboda ai maganar gani da ji ba a wasa da al’amarinsu ba, saboda suna taka muhimmiyar wajen bunkasa tattalin arziki kamar yadda Shugaban ya ce,da  ya tuna  da wani  tsarin kula da lafiya wanda ya aiwatar  mai suna tsarin “Jigi Bola”, wanda  aka aiwatar lokacin da yake wa’adinsa na farko a matsayinsa na gwamnan Jihar Legas a shekarar 2001 inda aka kula da lafiyar idanun mutane kyauta na al’ummar Legas, inda aka  bude sabon babi na kula da lafiyar al’umma a Afirka ta yamma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama
Manyan Labarai

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Next Post
Sabuwar Hanyar Kwacen Shafin Facebook (I)

Sabuwar Hanyar Kwacen Shafin Facebook (I)

LABARAI MASU NASABA

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.