• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shiru-Shiru Ba Tsoro Ba Ne…

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shiru-Shiru Ba Tsoro Ba Ne…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A duk lokacin da aka kira taruka kama daga na tattalin arziki, al’adu, ko wasanni ko Ilimi ko kare muhalli ko harkar tsaro, walau a mataki na kasa ko shiyya ko kasa da kasa, muhimman abubuwan da mahalarta tarukan ke tattaunawa, su ne matsaloli da nasarori da aka cimma a wadannan fannoni, gami da sabbin dabaru ko matakai da aka bijiro da su don inganta su, wadda daga karshe za su taimaka wajen haifar da kyakkyawan sakamako da ma burin da ake fatan cimmawa, wanda zai amfani duniya baki daya.

Sai dai wani abin mamaki shi ne, yayin taron tsaro na Shangri-La karo na 19 da ya gudana a kasar Singapore, maimakon a mayar da hankali kan yadda za a inganta matakan tsaro da zai amfani duniya baki daya, sai Amurka da wasu kawayenta suka mayar da hankali kawai wajen neman shafawa kasar Sin baken fenti da ma tsoma baki a harkokin cikin gidanta. Wannan ya sa ministan tsaron kasar Sin Wei Fenghe, yayin da yake gabatar da nasa jawabin a wajen taron, ya nunawa masu irin wannan mugun nufi kan kasar Sin cewa, shiru-shiru fa ba tsoro ba ne…

Sakon da minista Wei ya gabatar, ya kara tunatar da bangaren Amurka da ma duniya baki daya cewa, yanzu huldar da ke tsakanin kasashen 2 tana cikin wani muhimmin lokaci, kuma kyakkyawar huldar da ke tsakaninta da Amurka ta dace da muradunsu da ma duniya baki daya.

Amma idan har Amurka ta nace da neman tayar da rikici tsakaninta da Sin, to hakan ba zai kawo musu da ma kasashen duniya alheri ba. Haka kuma bai dace ba Amurka da kawayenta su rika ayyana kasar Sin a matsayin wai mai takara da Amurka ko barazana, idan kuma suka yi hakan, hakika za ta yi mummunan kuskure. Idan kunne ya ji, to gangan jiki ya tsira.

Kasar Sin dai ta bukaci Amurka da ta daina shafa mata kashin kaji, da neman dakile ci gaban ta, kana ta daina tsoma baki a harkokin cikin gidanta, da kuma illanta muradun kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Wani muhimmin batu da Amurka da sauran masu neman ballewar yankin Taiwan ya dace su fahimta da kunnen basira shi ne, sake hadewar Taiwan da babban yanki cikin lumana, shi ne babban fatan al’ummar Sinawa. Kuma duk wanda ya kuskura ya nemi tayar da batun ballewar yankin Taiwan daga kasar Sin, kasar Sin ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen mayar da duk wani martani ko ta halin kaka. Domin yaro bai san wuta ba, sai ya taka.

Masu fashin baki na kara jaddada cewa, wajibi ne Sin da Amurka su tattauna da juna, su mutunta juna, su kuma zauna tare cikin lumana, su hada kansu domin samun moriyar juna, amma idan Amurka ta nemi yin fito-na-fito da Sin, to, kasar Sin ta sha nanata cewa, ba za ta yarda a yi mata sakiyar da babu ruwa ba. (Ibrahim)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Yada Luwadi: Saudiyya Ta Hana Sayar Da Kayan Wasa Na Yara Masu Siffanta Jinsin Mutum

Next Post

NDLEA Ta Kwace Kwaya Mai Nauyin Kilo 4,520 A Jihar Zamfara

Related

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki
Daga Birnin Sin

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

13 hours ago
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

15 hours ago
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
Daga Birnin Sin

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

15 hours ago
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
Daga Birnin Sin

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

17 hours ago
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
Daga Birnin Sin

Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

17 hours ago
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

19 hours ago
Next Post
NDLEA Ta Kwace Kwaya Mai Nauyin Kilo 4,520 A Jihar Zamfara

NDLEA Ta Kwace Kwaya Mai Nauyin Kilo 4,520 A Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

July 31, 2025
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC

July 31, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

July 31, 2025
Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

July 31, 2025
Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

July 31, 2025
Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.