• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shiru-Shiru Ba Tsoro Ba Ne…

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shiru-Shiru Ba Tsoro Ba Ne…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A duk lokacin da aka kira taruka kama daga na tattalin arziki, al’adu, ko wasanni ko Ilimi ko kare muhalli ko harkar tsaro, walau a mataki na kasa ko shiyya ko kasa da kasa, muhimman abubuwan da mahalarta tarukan ke tattaunawa, su ne matsaloli da nasarori da aka cimma a wadannan fannoni, gami da sabbin dabaru ko matakai da aka bijiro da su don inganta su, wadda daga karshe za su taimaka wajen haifar da kyakkyawan sakamako da ma burin da ake fatan cimmawa, wanda zai amfani duniya baki daya.

Sai dai wani abin mamaki shi ne, yayin taron tsaro na Shangri-La karo na 19 da ya gudana a kasar Singapore, maimakon a mayar da hankali kan yadda za a inganta matakan tsaro da zai amfani duniya baki daya, sai Amurka da wasu kawayenta suka mayar da hankali kawai wajen neman shafawa kasar Sin baken fenti da ma tsoma baki a harkokin cikin gidanta. Wannan ya sa ministan tsaron kasar Sin Wei Fenghe, yayin da yake gabatar da nasa jawabin a wajen taron, ya nunawa masu irin wannan mugun nufi kan kasar Sin cewa, shiru-shiru fa ba tsoro ba ne…

Sakon da minista Wei ya gabatar, ya kara tunatar da bangaren Amurka da ma duniya baki daya cewa, yanzu huldar da ke tsakanin kasashen 2 tana cikin wani muhimmin lokaci, kuma kyakkyawar huldar da ke tsakaninta da Amurka ta dace da muradunsu da ma duniya baki daya.

Amma idan har Amurka ta nace da neman tayar da rikici tsakaninta da Sin, to hakan ba zai kawo musu da ma kasashen duniya alheri ba. Haka kuma bai dace ba Amurka da kawayenta su rika ayyana kasar Sin a matsayin wai mai takara da Amurka ko barazana, idan kuma suka yi hakan, hakika za ta yi mummunan kuskure. Idan kunne ya ji, to gangan jiki ya tsira.

Kasar Sin dai ta bukaci Amurka da ta daina shafa mata kashin kaji, da neman dakile ci gaban ta, kana ta daina tsoma baki a harkokin cikin gidanta, da kuma illanta muradun kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Wani muhimmin batu da Amurka da sauran masu neman ballewar yankin Taiwan ya dace su fahimta da kunnen basira shi ne, sake hadewar Taiwan da babban yanki cikin lumana, shi ne babban fatan al’ummar Sinawa. Kuma duk wanda ya kuskura ya nemi tayar da batun ballewar yankin Taiwan daga kasar Sin, kasar Sin ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen mayar da duk wani martani ko ta halin kaka. Domin yaro bai san wuta ba, sai ya taka.

Masu fashin baki na kara jaddada cewa, wajibi ne Sin da Amurka su tattauna da juna, su mutunta juna, su kuma zauna tare cikin lumana, su hada kansu domin samun moriyar juna, amma idan Amurka ta nemi yin fito-na-fito da Sin, to, kasar Sin ta sha nanata cewa, ba za ta yarda a yi mata sakiyar da babu ruwa ba. (Ibrahim)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Yada Luwadi: Saudiyya Ta Hana Sayar Da Kayan Wasa Na Yara Masu Siffanta Jinsin Mutum

Next Post

NDLEA Ta Kwace Kwaya Mai Nauyin Kilo 4,520 A Jihar Zamfara

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

16 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

17 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

19 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

20 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

1 day ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

1 day ago
Next Post
NDLEA Ta Kwace Kwaya Mai Nauyin Kilo 4,520 A Jihar Zamfara

NDLEA Ta Kwace Kwaya Mai Nauyin Kilo 4,520 A Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.