• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Tinubu Masoyin Arewa Ne – Gwamna Uba Sani

by Sulaiman
1 year ago
Uba sani

Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna ya yi Allah-wadai da ikirarin da ake yi na cewa, “Shugaba Tinubu na adawa da Arewa”, inda ya ce, karya ne, kuma ikirarin sam bai dace ba.

Ya bayyana hakan ne a wata ziyarar ban girma da sabbin shugabannin kungiyar tuntuba ta Arewa (ACF) suka kai a gidan gwamnati Kaduna, inda ya bayyana ikirarin a matsayin makircin wasu kwararrun ‘yan siyasa.

  • Sin Ta Kara Adadin Sabbin Guraben Ayyukan Yi Miliyan 6.98 A Rabin Farko Na Shekarar Bana 
  • ACF Ta Koka Da Rashin Tsaro Da Talauci A Arewa

A cewarsa, gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu tana ba gwamnatocin jihohin Arewa goyon baya irin wanda ba a saba gani ba don magance dimbin kalubalen da suke fuskanta.

 

Gwamnan ya ci gaba da bayyana cewa, dole ne masu ruwa da tsaki a Arewa su fada wa kansu gaskiya sannan su hada kai don samar da dabarun bai daya don magance kalubalen ci gaba, tare da tunkarar masu aikata laifuka da ke haddasa wa al’umma kuncin rayuwa.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

Uba sani

Ya yi nuni da cewa, sabon kwamitin zartaswa na ACF ya zo a daidai lokacin da ake fama da manyan kalubale da ke fuskantar yankin Arewa.

 

“Muna fuskantar matsaloli masu wuya game da sha’anin tsaro da ke hana ci gaba. Masu aikata laifuka sun mamaye al’ummomin Arewa suna wargaza ci gaban da ta samu ta fuskoki da dama. Rashin ci gaban mu (Yankin Arewa) yana da ban tsoro kuma yana buƙatar kulawa cikin gaggawa ”

Uba sani

Ya ci gaba da bayyana cewa, a bayyane yake cewa, Arewacin Nijeriya na fuskantar barazanar wanzuwa kuma lokaci ya yi da kowa ya kamata ya tashi tsaye wajen kawar da yankin daga durkushewa.

 

Gwamna Uba Sani ya jaddada cewa, ya kamata ‘yan Arewacin Nijeriya su daina zargin wane ne ko wacce ce matsalar Arewa, kamata ya yi a nemo ta yadda asalin matsalar ta faro.

 

“Mun kasa yi wa kanmu wasu muhimman tambayoyi. Ta ina matsalar ta faro a Arewa? Su wane ne masu hannu a cikin rashin ci gaban Arewa? Me muka yi a daidaiku da jama’a don nemo hanyoyin magance kalubalen da Arewa ke fuskanta?

 

A cewarsa, kungiyar tuntuba ta Arewa, ACF na da babban rawar da za ta taka wajen samar da matsayar da ake bukata domin ganin an shawo kan kalubale iri-iri da ke fuskantar Arewacin Nijeriya.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
Labarai

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai
Labarai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Next Post
Kasar Sin Tana Da Tashoshin 5G Miliyan 3.92

Kasar Sin Tana Da Tashoshin 5G Miliyan 3.92

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.