• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Tinubu Masoyin Arewa Ne – Gwamna Uba Sani

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Shugaba Tinubu Masoyin Arewa Ne – Gwamna Uba Sani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna ya yi Allah-wadai da ikirarin da ake yi na cewa, “Shugaba Tinubu na adawa da Arewa”, inda ya ce, karya ne, kuma ikirarin sam bai dace ba.

Ya bayyana hakan ne a wata ziyarar ban girma da sabbin shugabannin kungiyar tuntuba ta Arewa (ACF) suka kai a gidan gwamnati Kaduna, inda ya bayyana ikirarin a matsayin makircin wasu kwararrun ‘yan siyasa.

  • Sin Ta Kara Adadin Sabbin Guraben Ayyukan Yi Miliyan 6.98 A Rabin Farko Na Shekarar Bana 
  • ACF Ta Koka Da Rashin Tsaro Da Talauci A Arewa

A cewarsa, gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu tana ba gwamnatocin jihohin Arewa goyon baya irin wanda ba a saba gani ba don magance dimbin kalubalen da suke fuskanta.

 

Gwamnan ya ci gaba da bayyana cewa, dole ne masu ruwa da tsaki a Arewa su fada wa kansu gaskiya sannan su hada kai don samar da dabarun bai daya don magance kalubalen ci gaba, tare da tunkarar masu aikata laifuka da ke haddasa wa al’umma kuncin rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Uba sani

Ya yi nuni da cewa, sabon kwamitin zartaswa na ACF ya zo a daidai lokacin da ake fama da manyan kalubale da ke fuskantar yankin Arewa.

 

“Muna fuskantar matsaloli masu wuya game da sha’anin tsaro da ke hana ci gaba. Masu aikata laifuka sun mamaye al’ummomin Arewa suna wargaza ci gaban da ta samu ta fuskoki da dama. Rashin ci gaban mu (Yankin Arewa) yana da ban tsoro kuma yana buƙatar kulawa cikin gaggawa ”

Uba sani

Ya ci gaba da bayyana cewa, a bayyane yake cewa, Arewacin Nijeriya na fuskantar barazanar wanzuwa kuma lokaci ya yi da kowa ya kamata ya tashi tsaye wajen kawar da yankin daga durkushewa.

 

Gwamna Uba Sani ya jaddada cewa, ya kamata ‘yan Arewacin Nijeriya su daina zargin wane ne ko wacce ce matsalar Arewa, kamata ya yi a nemo ta yadda asalin matsalar ta faro.

 

“Mun kasa yi wa kanmu wasu muhimman tambayoyi. Ta ina matsalar ta faro a Arewa? Su wane ne masu hannu a cikin rashin ci gaban Arewa? Me muka yi a daidaiku da jama’a don nemo hanyoyin magance kalubalen da Arewa ke fuskanta?

 

A cewarsa, kungiyar tuntuba ta Arewa, ACF na da babban rawar da za ta taka wajen samar da matsayar da ake bukata domin ganin an shawo kan kalubale iri-iri da ke fuskantar Arewacin Nijeriya.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abubakar Sani BelloACFKaduna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yarjejeniyar Beijing: Mabudin Zaman Lafiya A Zirin Gaza

Next Post

Kasar Sin Tana Da Tashoshin 5G Miliyan 3.92

Related

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato
Labarai

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

1 hour ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

3 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

6 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

7 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

15 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

19 hours ago
Next Post
Kasar Sin Tana Da Tashoshin 5G Miliyan 3.92

Kasar Sin Tana Da Tashoshin 5G Miliyan 3.92

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.