ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Tinubu Masoyin Arewa Ne – Gwamna Uba Sani

by Sulaiman
2 years ago
Uba sani

Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna ya yi Allah-wadai da ikirarin da ake yi na cewa, “Shugaba Tinubu na adawa da Arewa”, inda ya ce, karya ne, kuma ikirarin sam bai dace ba.

Ya bayyana hakan ne a wata ziyarar ban girma da sabbin shugabannin kungiyar tuntuba ta Arewa (ACF) suka kai a gidan gwamnati Kaduna, inda ya bayyana ikirarin a matsayin makircin wasu kwararrun ‘yan siyasa.

  • Sin Ta Kara Adadin Sabbin Guraben Ayyukan Yi Miliyan 6.98 A Rabin Farko Na Shekarar Bana 
  • ACF Ta Koka Da Rashin Tsaro Da Talauci A Arewa

A cewarsa, gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu tana ba gwamnatocin jihohin Arewa goyon baya irin wanda ba a saba gani ba don magance dimbin kalubalen da suke fuskanta.

ADVERTISEMENT

 

Gwamnan ya ci gaba da bayyana cewa, dole ne masu ruwa da tsaki a Arewa su fada wa kansu gaskiya sannan su hada kai don samar da dabarun bai daya don magance kalubalen ci gaba, tare da tunkarar masu aikata laifuka da ke haddasa wa al’umma kuncin rayuwa.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Uba sani

Ya yi nuni da cewa, sabon kwamitin zartaswa na ACF ya zo a daidai lokacin da ake fama da manyan kalubale da ke fuskantar yankin Arewa.

 

“Muna fuskantar matsaloli masu wuya game da sha’anin tsaro da ke hana ci gaba. Masu aikata laifuka sun mamaye al’ummomin Arewa suna wargaza ci gaban da ta samu ta fuskoki da dama. Rashin ci gaban mu (Yankin Arewa) yana da ban tsoro kuma yana buƙatar kulawa cikin gaggawa ”

Uba sani

Ya ci gaba da bayyana cewa, a bayyane yake cewa, Arewacin Nijeriya na fuskantar barazanar wanzuwa kuma lokaci ya yi da kowa ya kamata ya tashi tsaye wajen kawar da yankin daga durkushewa.

 

Gwamna Uba Sani ya jaddada cewa, ya kamata ‘yan Arewacin Nijeriya su daina zargin wane ne ko wacce ce matsalar Arewa, kamata ya yi a nemo ta yadda asalin matsalar ta faro.

 

“Mun kasa yi wa kanmu wasu muhimman tambayoyi. Ta ina matsalar ta faro a Arewa? Su wane ne masu hannu a cikin rashin ci gaban Arewa? Me muka yi a daidaiku da jama’a don nemo hanyoyin magance kalubalen da Arewa ke fuskanta?

 

A cewarsa, kungiyar tuntuba ta Arewa, ACF na da babban rawar da za ta taka wajen samar da matsayar da ake bukata domin ganin an shawo kan kalubale iri-iri da ke fuskantar Arewacin Nijeriya.

 

Uba sani
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Kasar Sin Tana Da Tashoshin 5G Miliyan 3.92

Kasar Sin Tana Da Tashoshin 5G Miliyan 3.92

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.