Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gabatar da sakon jaje ga takwaransa na Pakistan Arif Alvi, bisa matsanaciyar ambaliyar ruwa da ta mamaye wasu sassan kasar ta Pakistan.
Tun daga watan Yuni ne ake ta tafka ruwan sama kamar da bakin kwarya a kasar, lamarin da ya haifar da ambaliyar ruwa da kawo yanzu ta sabbaba rasuwar mutane 1,061, kamar dai yadda hukumar yaki da bala’u ta kasar ta bayyana, cikin alkaluman da ta fitar a jiya Lahadi. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp