Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jaddada bukatar kara azama, a fannin ingiza matakan inganta lafiyar yara, da ci gaban su a dukkanin fannoni, yana mai mika gaisuwar sa ga daukacin yaran kasar Sin, albarkacin ranar yara ta kasa da kasa da ake yin bikin ta duk shekara, a ranar 1 ga watan Yuni.
Xi ya bayyana hakan ne cikin wasikar da ya aike ga cibiyar yara ta kasar Sin a yau Talata, a gabar da cibiyar ke bikin cika shekaru 40 da kafuwa.(Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp