• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Sin Ya Tattauna Da Takwaransa Na Cote d’Ivoire

by CMG Hausa
3 years ago
Shugaban Kasar Sin

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya tattauna ta wayar tarho da takwaransa na kasar Cote d’Ivoire, Alassane Ouattara, da yammacin yau Talata.

Yayin ganawar, Xi jinping ya bayyana Cote d’Ivoire a matsayin muhimmiyar abokiyar huldar kasar Sin a Afrika. Ya kuma bayyana cika shekaru 40 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu da za a yi a badi, a matsayin wanda ya cancanci bangarorin biyu su yi murna da shi. Haka kuma, ya ce Sin tana yabawa da yadda Cote d’Ivoire ke rungumar manufar kasar Sin daya tak a duniya, kana a shirye take ta hada kai da Cote d’Ivoire don su ci gaba da goyon bayan juna game da batutuwan da suka shafi muradunsu da zurfafa dangantakarsu zuwa wani sabon matsayi.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Bude Sabon Babin Aiwatar Da Dokokin Kundin Tsarin Mulkin Kasar A Sabon Zamani

A nasa bangare, shugaba Alassane Ouattara, ya ce yana da kyakkyawan fata game da cikar kasashen biyu shekaru 40 da kulla huldar diflomasiyya. A cewarsa, Sin ta taimakawa kasar gaya, kana ta bayar da muhimman gudunmuwa wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankuna da ma duniya baki daya, ciki har da Cote d’Ivoire.

Sannan, tana tallafawa ci gaban tattalin arziki da zamantakewar kasashen Afrika.

Shugaba Ouattara ya kuma jaddada cewa, kasarsa na nacewa ga manufar Sin daya tak, haka kuma tana goyon bayan tsarin huldar kasa da kasa da kuma shawarar Ziri Daya da Hanya Daya.

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Bugu da kari, a shirye Cote d’Ivoire take, ta ci gaba da karfafa hadin gwiwa da Sin karkashin tsarin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika na FOCAC, su kara tuntubar juna kan batutuwan yankuna da ma duniya.(Faeza Mustapha)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 
Daga Birnin Sin

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba
Daga Birnin Sin

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Next Post
Matakan Sin Na Yaki Da COVID-19 Sun Haifar Da Da Mai Ido

Matakan Sin Na Yaki Da COVID-19 Sun Haifar Da Da Mai Ido

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

October 22, 2025
Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

October 22, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.