ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakan Sin Na Yaki Da COVID-19 Sun Haifar Da Da Mai Ido

by CMG Hausa
4 years ago
COVID-19

Cibiyar yada shirye-shirye da harsunan Asiya da Afrika, na Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG, ya gudanar da wani taron karawa juna sani kan yanayin kasar Sin a kokarinta na dakile cutar COVID-19.

Idan ba a manta ba, kasar Sin ce kasa ta farko da ta sanar da bullar cutar a hukumance ga hukumar lafiya ta duniya a karshen shekarar 2019, duk da cewa, sakamakon tarin bincike sun nuna cewa, an samu bullar cutar a wurare da dama kafin a same ta a kasar Sin. Baya ga haka, har kawo yanzu, babu wata kasa da ta taka rawar gani wajen yaki da cutar kamar kasar ta Sin.

  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da “Bikin Nuna Al’adun Larabawa”

Wasu kafafen yada labarai na yammacin duniya da ma gwamnatocinsu, sun yi ta yada jita-jitar cewa, matakan kasar Sin sun take hakkokin bil adama.

ADVERTISEMENT

Sai dai akasin abun da suke nufi, matakan kasar Sin sun cancanci jinjina matuka, domin sun taka rawar gani wajen kare al’umma daga rasa rayukansu sanadiyyar kamuwa da cutar, haka kuma sun kare yaduwar cutar daga kasar zuwa sauran sassan duniya. Gani ya kori ji, domin duk wani dake kasar Sin zai bada shaidar cewa, matakan sun taka rawar gani. Idan kuma aka duba su kasashen masu yada jita jitar, har yanzu ba su kama kafar Sin wajen yaki da cutar ba, haka kuma suna fama da matsalolin tattalin arziki.

Yadda CMG ya shirya wannan taro, hakika zai kara wayar da kan al’ummomin Afrika kan illolin dake tattare da annobar da ma yadda za su kare kawunansu, da kuma dalilan Sin din na daukar matakan da ta dauka, tare da wayar musu da kai daga karai-rayi ko jita-jita da aka yi ta yadawa dangane da su. Baya ga haka, zai zama darasi ta yadda gwamnatocin kasashen za su iya shiryawa tunkarar annoba da mai yuwuwa ka iya barkewa a nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Duk da cewa, ana ganin Sin ta dauki tsauraran matakai, matakan nata sun haifar da da-mai-ido, ta cimma dimbin nasarori, domin ita ce kasa daya tilo da ta samu ci gaban tattalin arziki bayan bullar annobar, haka kuma ita ce ta bayar da gudunmawa ga ci gaban tattalin arzikin duniya.

Haka zalika, wadannan kyawawan manufofi ne ya sa ake ganin yayin da ci gaban kasashen duniya zai gamu da cikas a shekarar 2023, an yi hasashen tattalin arzikin kasar Sin zai farfado tare da kara kuzari. Ingantattun manufofin kudi da Sin ta dauka da kuma saukaka matakan yaki da annobar da ta yi a baya-bayan nan, za su taimaka wajen samun habakar tattalin arzikinta wanda zai ci gaba da bayar da gudunmawa ga tattalin arzikin duniya baki daya. Haka kuma, zai kara bunkasa harkokin cinikayya da mu’amala da ma musaya da kasashe masu tasowa aminanta, musammam ma na Afrika.

COVID-19
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
Daga Birnin Sin

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
Daga Birnin Sin

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Next Post
Sinawa Suna Tinkarar COVID-19 Da Karfin Gwiwa

Sinawa Suna Tinkarar COVID-19 Da Karfin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.