ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakan Sin Na Yaki Da COVID-19 Sun Haifar Da Da Mai Ido

by CMG Hausa
3 years ago
COVID-19

Cibiyar yada shirye-shirye da harsunan Asiya da Afrika, na Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG, ya gudanar da wani taron karawa juna sani kan yanayin kasar Sin a kokarinta na dakile cutar COVID-19.

Idan ba a manta ba, kasar Sin ce kasa ta farko da ta sanar da bullar cutar a hukumance ga hukumar lafiya ta duniya a karshen shekarar 2019, duk da cewa, sakamakon tarin bincike sun nuna cewa, an samu bullar cutar a wurare da dama kafin a same ta a kasar Sin. Baya ga haka, har kawo yanzu, babu wata kasa da ta taka rawar gani wajen yaki da cutar kamar kasar ta Sin.

  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da “Bikin Nuna Al’adun Larabawa”

Wasu kafafen yada labarai na yammacin duniya da ma gwamnatocinsu, sun yi ta yada jita-jitar cewa, matakan kasar Sin sun take hakkokin bil adama.

ADVERTISEMENT

Sai dai akasin abun da suke nufi, matakan kasar Sin sun cancanci jinjina matuka, domin sun taka rawar gani wajen kare al’umma daga rasa rayukansu sanadiyyar kamuwa da cutar, haka kuma sun kare yaduwar cutar daga kasar zuwa sauran sassan duniya. Gani ya kori ji, domin duk wani dake kasar Sin zai bada shaidar cewa, matakan sun taka rawar gani. Idan kuma aka duba su kasashen masu yada jita jitar, har yanzu ba su kama kafar Sin wajen yaki da cutar ba, haka kuma suna fama da matsalolin tattalin arziki.

Yadda CMG ya shirya wannan taro, hakika zai kara wayar da kan al’ummomin Afrika kan illolin dake tattare da annobar da ma yadda za su kare kawunansu, da kuma dalilan Sin din na daukar matakan da ta dauka, tare da wayar musu da kai daga karai-rayi ko jita-jita da aka yi ta yadawa dangane da su. Baya ga haka, zai zama darasi ta yadda gwamnatocin kasashen za su iya shiryawa tunkarar annoba da mai yuwuwa ka iya barkewa a nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

Duk da cewa, ana ganin Sin ta dauki tsauraran matakai, matakan nata sun haifar da da-mai-ido, ta cimma dimbin nasarori, domin ita ce kasa daya tilo da ta samu ci gaban tattalin arziki bayan bullar annobar, haka kuma ita ce ta bayar da gudunmawa ga ci gaban tattalin arzikin duniya.

Haka zalika, wadannan kyawawan manufofi ne ya sa ake ganin yayin da ci gaban kasashen duniya zai gamu da cikas a shekarar 2023, an yi hasashen tattalin arzikin kasar Sin zai farfado tare da kara kuzari. Ingantattun manufofin kudi da Sin ta dauka da kuma saukaka matakan yaki da annobar da ta yi a baya-bayan nan, za su taimaka wajen samun habakar tattalin arzikinta wanda zai ci gaba da bayar da gudunmawa ga tattalin arzikin duniya baki daya. Haka kuma, zai kara bunkasa harkokin cinikayya da mu’amala da ma musaya da kasashe masu tasowa aminanta, musammam ma na Afrika.

COVID-19
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Next Post
Sinawa Suna Tinkarar COVID-19 Da Karfin Gwiwa

Sinawa Suna Tinkarar COVID-19 Da Karfin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.