A gabannin bikin Bazara bisa kalandar gargajiyar kasar Sin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai rangadin aiki a birnin Tianjin da ke arewacin kasar Sin, inda ya gana da jami’an kananan hukumomi da fararen hula.
A safiyar ranar 1 ga watan Faburairu, ya ziyarci kauyen Diliubu na garin Xinku na yankin Xiqing dake birnin, inda ya duba yadda ake farfado da aikin noma bayan aukuwar ambaliyar ruwa a shekarar bara, da ganawa da mazauna wurin da bala’in ya shafa. Da yamma kuma, ya je titin al’adun gargajiya dake birnin, inda ya duba yadda ake samar da kayayyaki a kasuwa a gabannin bikin Bazara, biki mafi muhimmanci ga al’ummar Sinawa, da kuma yadda ake kiyaye unguwar al’adu mai dogon tarihi. (Tasallah Yuan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp