ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Tana Murnar Mummunar Ribar Da Ta Ci

by CGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Gwamnatin kasar Amurka da kamfanonin samar da makaman soja na kasar sun kara cin mummunar riba.

A ranar 29 ga wata, ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Amurka ta bayar da sanarwar cewa, a shekarar 2023, kudin makaman soja da ta sayar ga kasashen ketare ya karu da kaso 16%, adadin da ya kai har dalar Amurka biliyan 238. Kafin wannan, alkaluman da cibiyar nazari ta SIPRI da ke birnin Stockholm ta samar sun shaida cewa, daga shekarar 2018 zuwa ta 2022, yawan makaman da kasar Amurka ta fitar zuwa ketare ya dau kaso 40% na dukkanin makaman da aka fitar a fadin duniya, adadin da ya karu da kashi 7% bisa na tsakanin shekarar 2013 da ta 2017.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Yi Rangadi A Tianjin 
  • Karuwar Rincabewar Tsaro: Manyan Hafsoshi Sun Shiga Tsaka Mai Wuya

Hakan ya faru ne sakamakon yadda Amurka ta yi ta rura rikici a fadin duniya don cin mummunar riba, matakin da ya lalata zaman lafiya a duniya. Rahoton da cibiyar nazari ta Cato ta kasar Amurka ta fitar ya yi nuni da cewa, daga shekarar 2012 zuwa ta 2022, Amurka ta sayar da manyan makamai da kudinsu ya kai dala biliyan 16 ga kasashe da shiyyoyi 28 da ke fama da rikici a duniya. Bayan barkewar rikici tsakanin Palasdinu da Isra’ila a wannan karo, Amurka ba ma kawai ta gaggauta samar da gudummawar soja ga Isra’ila ba, har ma ta sayar da makaman soja ga Isra’ila din har sau biyu a watan Disamban bara, kuma ba tare da an tattauna batun a majalisar dokokin kasar ba. Ban da haka, a bara, Amurka ta ci gaba da rura wutar rikicin Ukraine. Tun bayan barkewar rikicin a watan Faburairun shekarar 2022, Amurka ta riga ta samar da gudummawar da ta zarce dala biliyan 110 ga Ukraine din. A shirin kasafin kudi na bana da gwamnatin Biden ta gabatar, an ware dala biliyan 106 ta fannin samar da gudummawar soja ga Isra’ila da Ukraine da sauransu.

ADVERTISEMENT

Sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken ya bayyana a fili cewa, “A hakika kaso 90% na kudin gudummawar soja da muka samarwa Ukraine, an kashe su ne a cikin gidan Amurka, ta fannonin masu samar da kayanmu, kuma hakan ya kara samar da guraben aikin yi ga Amurkawa, tare da sa kaimin bunkasuwar tattalin arzikinmu.” To, dalili ke nan da ya sa Amurka ke matukar sha’awar tada rikci a duniya.

Ba da jimawa ba bayan barkewar rikicin Ukraine, mista Franklin C. Spinney wanda ya shafe shekaru da dama yana aiki a ofishin ministan tsaron kasar Amurka ya rubuta cewa, rikicin Rasha da Ukraine “ya sa mutane da yawa a ma’aikatar tsaron kasar Amurka ta Pentagon da masana’antun samar da makamai na kasar da ma majalisar dokokin kasar sun taya juna murna asirce. ” Abin haka yake, abin da ke faruwa a kasashen da ke fama da rikici, ba kome ba ne ga ‘yan siyasar kasar Amurka da ma sojoji da masana’antun samar da makamai na kasar, sabo da mummunar riba mai tsoka da suka ci. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Cire Tallafin Man Fetur: Minista Ya Yaba Wa IPMAN Don Rungumar Shirin CNG

Cire Tallafin Man Fetur: Minista Ya Yaba Wa IPMAN Don Rungumar Shirin CNG

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.