ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Tana Murnar Mummunar Ribar Da Ta Ci

by CGTN Hausa
3 years ago
Amurka

Gwamnatin kasar Amurka da kamfanonin samar da makaman soja na kasar sun kara cin mummunar riba.

A ranar 29 ga wata, ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Amurka ta bayar da sanarwar cewa, a shekarar 2023, kudin makaman soja da ta sayar ga kasashen ketare ya karu da kaso 16%, adadin da ya kai har dalar Amurka biliyan 238. Kafin wannan, alkaluman da cibiyar nazari ta SIPRI da ke birnin Stockholm ta samar sun shaida cewa, daga shekarar 2018 zuwa ta 2022, yawan makaman da kasar Amurka ta fitar zuwa ketare ya dau kaso 40% na dukkanin makaman da aka fitar a fadin duniya, adadin da ya karu da kashi 7% bisa na tsakanin shekarar 2013 da ta 2017.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Yi Rangadi A Tianjin 
  • Karuwar Rincabewar Tsaro: Manyan Hafsoshi Sun Shiga Tsaka Mai Wuya

Hakan ya faru ne sakamakon yadda Amurka ta yi ta rura rikici a fadin duniya don cin mummunar riba, matakin da ya lalata zaman lafiya a duniya. Rahoton da cibiyar nazari ta Cato ta kasar Amurka ta fitar ya yi nuni da cewa, daga shekarar 2012 zuwa ta 2022, Amurka ta sayar da manyan makamai da kudinsu ya kai dala biliyan 16 ga kasashe da shiyyoyi 28 da ke fama da rikici a duniya. Bayan barkewar rikici tsakanin Palasdinu da Isra’ila a wannan karo, Amurka ba ma kawai ta gaggauta samar da gudummawar soja ga Isra’ila ba, har ma ta sayar da makaman soja ga Isra’ila din har sau biyu a watan Disamban bara, kuma ba tare da an tattauna batun a majalisar dokokin kasar ba. Ban da haka, a bara, Amurka ta ci gaba da rura wutar rikicin Ukraine. Tun bayan barkewar rikicin a watan Faburairun shekarar 2022, Amurka ta riga ta samar da gudummawar da ta zarce dala biliyan 110 ga Ukraine din. A shirin kasafin kudi na bana da gwamnatin Biden ta gabatar, an ware dala biliyan 106 ta fannin samar da gudummawar soja ga Isra’ila da Ukraine da sauransu.

ADVERTISEMENT

Sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken ya bayyana a fili cewa, “A hakika kaso 90% na kudin gudummawar soja da muka samarwa Ukraine, an kashe su ne a cikin gidan Amurka, ta fannonin masu samar da kayanmu, kuma hakan ya kara samar da guraben aikin yi ga Amurkawa, tare da sa kaimin bunkasuwar tattalin arzikinmu.” To, dalili ke nan da ya sa Amurka ke matukar sha’awar tada rikci a duniya.

Ba da jimawa ba bayan barkewar rikicin Ukraine, mista Franklin C. Spinney wanda ya shafe shekaru da dama yana aiki a ofishin ministan tsaron kasar Amurka ya rubuta cewa, rikicin Rasha da Ukraine “ya sa mutane da yawa a ma’aikatar tsaron kasar Amurka ta Pentagon da masana’antun samar da makamai na kasar da ma majalisar dokokin kasar sun taya juna murna asirce. ” Abin haka yake, abin da ke faruwa a kasashen da ke fama da rikici, ba kome ba ne ga ‘yan siyasar kasar Amurka da ma sojoji da masana’antun samar da makamai na kasar, sabo da mummunar riba mai tsoka da suka ci. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Amurka
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Cire Tallafin Man Fetur: Minista Ya Yaba Wa IPMAN Don Rungumar Shirin CNG

Cire Tallafin Man Fetur: Minista Ya Yaba Wa IPMAN Don Rungumar Shirin CNG

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.