Shugaban kasar Sin Xi Jinping, zai halarci bikin bude taron ministoci karo na 10 na dandalin tattauna hadin kan Sin da kasashen Larabawa da za a yi a ranar 30 ga watan Mayu, a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin, Hua Chunying ce ta sanar da hakan a yau Lahadi, inda ta ce shugaba Xi Jinping zai kuma gabatar da jawabi yayin bikin. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp