• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kwamitin Tsaro Ya Yi Murabus Kan Zargin Alaka Da ‘Yan Bindiga A Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kanar Garba Moyi ya yi murabus daga shugabancin kwamitin kirkiro da jami’an tsaro na Jihar Sakkwato kasa da mako daya da Gwamna Ahmed Aliyu ya nada shi mukamin.

Tsohon jami’in soji kana tsohon Kwamishinan Tsaro a Gwamnatin Tambuwal ya ajiye mukamin ne a kashin kan sa a bisa zargin da ake yi masa na cewar yana da hannu a sha’anin ta’addanci a Jihar kamar yadda ya bayyana a taron manema labarai a Sakkwato.

Jim kadan da Gwamnatin Sakkwato ta dora masa alhakin jagorantar kwamitin assasa rundunar tsaro ta jiha wadda za ta marawa kokarin hukumomin tsaro baya wajen yaki da ta’addanci a Jihar ne dimbin jama’a suka rika bayyana mabambantan ra’ayoyi kan cancanta da rashin cancntar tsohon sojan a aikin kwamitin samar da tsaro.

Fitattun Malamman Addinin Musulunci a Sakkwato, Sheikh Musa Ayuba Lukuwa da Murtala Assada duka a faifan bidiyo daban-daban sun bayyana karara cewar babban kuskure ne hannun ta kwamitin tsaro a hannun wanda aka jima ana zargin alakarsa da ‘yan ta’adda tare da sa hannu wajen hana al’umma bacci da idanu biyu, don haka suka bukaci Gwamnati ta canza shi.

A taron na manema labarai, Moyi ya bayyana cewar ajiye mukamin shine maslaha a gare shi domin kare kima da mutuncinsa ya fi gaban kowane irin mukami.

Labarai Masu Nasaba

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Ya ce yana da tarihin sadaukar da kai wajen bautawa kasa tare da ritaya a kashin kan sa bayan kwashe shekaru 35 a aikin soji a mukamin Kanar tare da shiga harkokin siyasa a in da ya fara da zama Shugaban Karamar Hukumar Isa. Ya ce jajircewarsa ga ci gaba da kyautata jin dadin jama’arsa ne dalilin da ya sa Gwamnatin Tambuwal ta nada shi Kwamishinan Tsaro, mukamin da a kashin kansa ya ajiye kafin karshen wa’adin mulkin tare da canza jam’iyya.

A cewarsa bisa ga sadaukarwarsa ne da sanin harkokin tsaro Gwamnatin Sakkwato ta nada shi mukamin shugabancin kwamitin. “A yau ina sanar da al’umma cewar na ajiye wannan mukamin a kashin kai na domin tabbatar da zaman lafiya da hadin kan al’umma.” Ya bayyana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin ZamfaraSokotoYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dabi’ar Saba Alkawarin Da Maza Ke Yi Ga Matan Da Za Su Aura

Next Post

Kasar Sin Ta Bukaci Tsagaita Wuta Da Samar Da Agajin Jin Kai A Zirin Gaza

Related

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

5 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

7 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

10 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

11 hours ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

11 hours ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

12 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Bukaci Tsagaita Wuta Da Samar Da Agajin Jin Kai A Zirin Gaza

Kasar Sin Ta Bukaci Tsagaita Wuta Da Samar Da Agajin Jin Kai A Zirin Gaza

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.