ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kwamitin Tsaro Ya Yi Murabus Kan Zargin Alaka Da ‘Yan Bindiga A Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
Tsaro

Kanar Garba Moyi ya yi murabus daga shugabancin kwamitin kirkiro da jami’an tsaro na Jihar Sakkwato kasa da mako daya da Gwamna Ahmed Aliyu ya nada shi mukamin.

Tsohon jami’in soji kana tsohon Kwamishinan Tsaro a Gwamnatin Tambuwal ya ajiye mukamin ne a kashin kan sa a bisa zargin da ake yi masa na cewar yana da hannu a sha’anin ta’addanci a Jihar kamar yadda ya bayyana a taron manema labarai a Sakkwato.

Jim kadan da Gwamnatin Sakkwato ta dora masa alhakin jagorantar kwamitin assasa rundunar tsaro ta jiha wadda za ta marawa kokarin hukumomin tsaro baya wajen yaki da ta’addanci a Jihar ne dimbin jama’a suka rika bayyana mabambantan ra’ayoyi kan cancanta da rashin cancntar tsohon sojan a aikin kwamitin samar da tsaro.

ADVERTISEMENT

Fitattun Malamman Addinin Musulunci a Sakkwato, Sheikh Musa Ayuba Lukuwa da Murtala Assada duka a faifan bidiyo daban-daban sun bayyana karara cewar babban kuskure ne hannun ta kwamitin tsaro a hannun wanda aka jima ana zargin alakarsa da ‘yan ta’adda tare da sa hannu wajen hana al’umma bacci da idanu biyu, don haka suka bukaci Gwamnati ta canza shi.

A taron na manema labarai, Moyi ya bayyana cewar ajiye mukamin shine maslaha a gare shi domin kare kima da mutuncinsa ya fi gaban kowane irin mukami.

LABARAI MASU NASABA

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

Ya ce yana da tarihin sadaukar da kai wajen bautawa kasa tare da ritaya a kashin kan sa bayan kwashe shekaru 35 a aikin soji a mukamin Kanar tare da shiga harkokin siyasa a in da ya fara da zama Shugaban Karamar Hukumar Isa. Ya ce jajircewarsa ga ci gaba da kyautata jin dadin jama’arsa ne dalilin da ya sa Gwamnatin Tambuwal ta nada shi Kwamishinan Tsaro, mukamin da a kashin kansa ya ajiye kafin karshen wa’adin mulkin tare da canza jam’iyya.

A cewarsa bisa ga sadaukarwarsa ne da sanin harkokin tsaro Gwamnatin Sakkwato ta nada shi mukamin shugabancin kwamitin. “A yau ina sanar da al’umma cewar na ajiye wannan mukamin a kashin kai na domin tabbatar da zaman lafiya da hadin kan al’umma.” Ya bayyana.

Tsaro
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto-2/
    Ƴan Gudun Hijira 43,000 Sun Amfana da Tallafin Gwamnatin Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto-2/
    Mata Ne Ginshikin Ci-Gaban Al’umma – Gimbiyar Dange
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto-2/
    BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto-2/
    Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni

MASU ALAKA

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro
Manyan Labarai

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

September 11, 2026
Tsaro
Manyan Labarai

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Tsaro
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Bukaci Tsagaita Wuta Da Samar Da Agajin Jin Kai A Zirin Gaza

Kasar Sin Ta Bukaci Tsagaita Wuta Da Samar Da Agajin Jin Kai A Zirin Gaza

LABARAI MASU NASABA

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

September 11, 2026
Sanata yari

Gwarzon Ɗan Siyasa Na Shekarar 2026 Sanata Abdul’Aziz Abubakar Yari

September 11, 2026
Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 11, 2026
SAW

Ɗabi’un Annabi (SAW) Kan Abubuwa Na Al’adar Rayuwa

September 11, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Horar Da Malamai 250,000

Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Horar Da Malamai 250,000

September 11, 2026
Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 13 Da ’Yan Bindiga Suka Yi Garkuwa Da Su

September 11, 2026
Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

September 11, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Tsaro

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Tsaro

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.