Shugaban tarayyar Najeriya Bola Tinubu, ya kaddamar da aikin samar da ruwan sha mai tsafta wanda kamfanin CGCOC na kasar Sin ya tallafa wajen gudanar da shi a birnin Abuja, fadar mulkin kasar. Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa, ta yin aiki tukuru a fannin samar da ababen more rayuwa, da kai tsaye za su inganta rayuwar al’ummun kasar.
Shugaba Tinubu ya bayyana aikin a matsayin muhimmin mataki na tabbatar da al’ummun birnin sun samu ruwa mai tsafta, mai dorewa kuma isasshen a gidaje da hukumomi, da dukkanin sassan birnin. Ya kuma godewa gwamnatin kasar Sin da kamfanin CGCOC, bisa hadin gwiwarsu wajen tabbatar da nasarar aikin.
Yayin da yake nasa tsokaci kuwa a bikin kaddamar da aikin, mukaddashin jakadan Sin a Najeriya Zhang Yi, ya ce aikin na da matukar muhimmanci ga kyautata samar da ruwa a birnin Abuja, kasancewar zai kara yawan ruwan da al’ummar birnin za su iya amfani da shi da rubi uku, wato daga kyubik mita 240,000 zuwa kyubik mita 720,000. Zai kuma baiwa al’ummun birnin har kimanin miliyan uku damar samun isasshen ruwa mai tsafta domin amfanin yau da kullum.
Bugu da kari, karkashin aikin, an horar da ma’aikata ‘yan kasa dabarun samar da ruwa, da fasahohin shimfida bututai, wanda hakan ya samar da guraben ayyukan yi na kai tsaye da wadanda ba na kai tsaye ba har sama da 3,000, matakin da ya ingiza fannin bunkasa kwarewa, da ciyar da tattalin arziki gaba, da ma raya zamantakewar al’ummar birnin na Abuja, kamar dai yadda kamfanin CGC Nigeria, reshen kamfanin CGCOC ya bayyana. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp