• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Ƙarin Girma Ga Jami’ai 4,526

by yahuzajere
3 years ago
NIS

LABARAI MASU NASABA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa, Isah Jere Idris ya sanar da ƙarin girma ga jami’an hukumar su 4,526 da suka yi jarrabawar ƙarin girma da waɗanda suka samu horaswa daban-daban ta ɗaga darajar muƙami a shekarar 2021.
  • “Ba Zan Mara Wa Atiku Ko Wani Dan Takara Na Kyale Tinubu Ba” —Buhari
Tabbatar da ƙarin girman na ƙunshe ne a cikin wasiƙar da ta zo daga Hukumar Gudanarwar Rundunonin da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Cikin Gida da aka yi wa lambar CDCFIB/S.33/VOLIII/54 mai ɗauke da kwanan wata,18 ga Agusta, 2022.
NIS
Shugaban hukumar ya bayyana hakan ne a yau a hedikwatarta yayin da yake yi wa wasu jami’ai masu taimaka masa  da ke cikin ma’aikatan da aka yi wa ƙarin girma ado da sabbin muƙamansu.
NIS
Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulɗa da jama’a na NIS, wanda shi ma aka ƙara masa girma daga ƙaramin Mataimakin Kwanturola (ACI) zuwa Babban Mataimakin kwanturola (DCI), Amos Okpu, ta ce jami’ai masu muƙamin ƙaramin mataimakan Kwanturola 145 sun samu ƙarin girma zuwa Babban Mataimakin Kwanturolan Shige da Fice; sannan masu muƙamin Babban Sufiritanda 99 sun samu ƙarin girma zuwa ƙaramin mataimakin Kwanturola.
Bugu da ƙari, akwai masu muƙamin Sufiritanda 307 da aka mayar da su matsayin Babban Sufiritanda; kana mataimakan Sufiritanda 338 sun samu ci gaba zuwa matsayin Sufiritanda.
NIS
Sauran waɗanda suka samu ƙarin girman su ne jami’ai 589 da aka ciyar da su gaba zuwa muƙamin mataimakin Sufiritanda na ɗaya (I), sai wasu  794 da aka ƙara musu muƙami zuwa Mataimakan Sufiritanda na biyu (II).
Har ila yau takardar ta yi bayanin cewa,
jami’ai masu muƙamin Sufeto 21 sun samu ci gaba zuwa mataimakin Sufiritanda na biyu (II). Yayin da wasu jami’ai 1254 suka sami ci gaba zuwa matsayi na Mataimakin Sufeto na biyu (II), kana akwai jimillar ƙananan jami’ai 979 da suka samu ƙwarewar aiki da aka ɗaga darajarsu zuwa matsayi na Mataimakin Sufiritanda na biyu.
NIS
Da yake jawabi a wajen bikin adonta muƙarrabansa, Shugaban NIS CGI Isah Jere Idris ya yaba wa Ministan Harkokin Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola wanda kuma ya zama shugaban hukumar gudanarwar rundunonin da ke ƙarƙashin ma’aikatar bisa jajircewarsa wajen ciyar da ma’aikata gaba.
Ya bukaci sabbin jami’an da aka kara musu girma da su ƙara ƙwazo da saka karamcin da aka yi musu ta hanyar sadaukarwa da kuma biyayya a bakin aiki.
Ya kuma bai wa gwamnati tabbacin cewa hukumar a ƙarƙashinsa za ta ci gaba da bayar da gudunmawa mai amfani ga zaman lafiya da ci gaban kasa.
NIS
Daga cikin jami’an da aka yi wa ado da sabbin mukamansu akwai Jami’in hulɗa da jama’a na NIS Amos OKPU, wanda aka ƙara wa girma zuwa DCI; da Jami’in kula da tsare-tsare na Kwanturola Janar MY Dutse mai barin gado da magajinsa MA Ajimobi wanda a yanzu suka zama Manyan Mataimakan Kwanturola.
NIS
Sauran sun haɗa da Mercy Gadzama, Manajar Kula da Cibiyar Fasaha ta NIS, da a yanzu ta zama Babbar Sufiritanda, da Jami’in Tsaro na Kwanturola Janar AO Olukoya, da aka kara masa girma zuwa muƙamin Babban Sufiritanda da Tanko Godiya da Nguar Loice Titus na Sashen Kai Ɗaukin Gaggawa (RRS), duka biyu da aka ƙara musu girma zuwa mataimakan Sufiritanda na Shige da Fice (II).
ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma
Labarai

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Next Post
kenya

Darussa Ga Nijeriya Daga Zaben Kasar Kenya

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.