• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Timor-Leste Da Firaministar Italiya

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugaban Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Timor-Leste Da Firaministar Italiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Timor-Leste Jose Ramos-Horta da firaministar kasar Italiya Giorgia Meloni wadanda suke ziyarar aiki a birnin Beijing, fadar mulkin Sin, a yau Litinin daya bayan daya.

 

Lokacin da yake ganawa da Jose Ramos-Horta, shugaban kasar Timor-Leste, Xi Jinping ya ce, kasar Sin a shirye take ta karfafa alaka da dabarun raya kasa da kasar Timor-Leste, da kuma taimaka mata wajen samun ‘yancin kai na tattalin arziki da bunkasuwa a fannoni daban daban.

  • Wang Yi Ya Bayyana Matsayin Kasar Sin Kan Batun Tekun Kudancin Kasar
  • Sin Da Amurka Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna A Dukkanin Matakai

A nasa bangare, Ramos-Horta ya ce, Timor-Leste yana goyon bayan duk kokarin da kasar Sin ke yi na kare ikon mallakar kasa da cikakken yankinta.

 

Labarai Masu Nasaba

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Bayan tattaunawar, shugabannin kasashen biyu sun shaida rattaba hannu kan shirin hadin gwiwa kan aikin gina “shawarar ziri daya da hanya daya” tare da wasu takardun hadin gwiwar kasashen biyu a fannonin aikin gona, da kiyaye muhalli, da tattalin arzikin dijital, sufurin jiragen sama, da dai sauransu, bangarorin biyu sun fitar da “sanarwar hadin gwiwa na jamhuriyar jama’ar kasar Sin da jamhuriyar dimokaradiyyar Timor-Leste kan zurfafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare”.

Sin

Sannan a lokacin da yake tattaunawa da firaministar kasar Italiya Giorgia Meloni, shugaba Xi, ya ce kasarsa da Italiya na kan iyakokin karshe na tsohuwar hanyar siliki, kuma kawancen musamman na tsawon lokaci tsakanin kasashen biyu ya samar da babbar gudummawa ga daukacin musaya, da koyi da juna tsakanin wayewar kan gabashi da yammacin duniya, tare da tallafawa ci gaban bil adama.

 

Shugaban na Sin ya kara da cewa, ruhin hanyar siliki na zaman lafiya da hadin gwiwa, da yin komai a bude, da tafiya tare da dukkanin sassa, da koyi da juna, da cimma moriyar juna, sun kasance wata haja mai kima da Sin da Italiya suka raba tsakanin su.

 

Daga nan shugaba Xi ya ce kamata ya yi sassan biyu su goyi baya, da yayata ruhin hanyar siliki, su nazarci tare da bunkasa alakar dake tsakanin su ta mahangar tarihi, da burin cimma nasara ta tsawon lokaci, tare da ingiza alakar su bisa daidaito. (Mohammed Yahaya, Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NCC Ta Umarci Kamfanonin Sadarwa Su Gaggauta Sake Haɗa Layukan Wayar Da Aka Katse  Saboda NIN-SIM

Next Post

Zanga-Zanga: Sojoji Sun Karɓe Iko Da Tsaron Hanyar Shiga Abuja

Related

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

5 minutes ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

1 hour ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

2 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

3 hours ago
Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 
Daga Birnin Sin

Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

4 hours ago
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

22 hours ago
Next Post
Zanga-Zanga: Sojoji Sun Karɓe Iko Da Tsaron Hanyar Shiga Abuja

Zanga-Zanga: Sojoji Sun Karɓe Iko Da Tsaron Hanyar Shiga Abuja

LABARAI MASU NASABA

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

August 22, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

August 22, 2025
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

August 22, 2025
Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

August 22, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.