• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Kasashen Habasha Da Kenya Sun Gana Da Wang Yi

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugabannin Kasashen Habasha Da Kenya Sun Gana Da Wang Yi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Firaministan Habasha Abiy Ahmed, ya gana da daraktan ofishin kula da harkokin waje na kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin (JKS) Wang Yi jiya Jumma’a, inda bangarorin biyu suka yi alkawarin inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.

Wang Yi ya kai ziyara kasar Habasha ne a kan hanyarsa ta hakartar taron masu ba da shawara kan harkokin tsaron kasa na kasashen BRICS karo na 13, da zai gudana a birnin Johannesburg na Afirka ta Kudu.

  • Masani Habasha Ya Yi Karin Haske Kan Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

A yayin ganawarsa da Wang, Abiy Ahmed ya yi karin haske kan manyan nasarorin da kasar Sin ta cimma, yayin da take bin tafarkin gurguzu mai sigar musamman na kasar Sin, yana mai cewa, ya yaba da yadda kasar Sin take nacewa kan tafarkin ci gaba da ya dace da yanayin kasarta, gami da saurin bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewa da ta samu, wanda ya zama abin koyi ga ragowar kasashe masu tasowa.

A nasa bangaren kuwa, Wang Yi ya bayyana cewa, Habasha babbar kasa ce a nahiyar Afirka da ke da tasiri mai mahimmanci. Yana mai cewa a matsayinsu na abokan huldar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare, Sin da Habasha suna da buri daya, kuma sun gudanar da hadin gwiwa mai inganci bisa tsare-tsare irin su “shawarar ziri daya da hanya daya” da dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka, wanda ke jagorantar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka.

Ban da haka, Wang Yi shi ma ya gana da mataimakin firaministan kasar Habasha kuma ministan harkokin wajen kasar Demeke Mekonnen.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Yayin ganawar, Wang ya ce, kasar Sin tana goyon bayan kasar Habasha wajen kiyaye ikonta mulkin da cikakkun yankunanta, da goyon bayan kasar wajen cika alkawarin da ta dauka na tabbatar da hadin kai da zaman lafiyar kasar, tana kuma goyon bayanta wajen taka muhimmiyar rawa a harkokin shiyya-shiyya da na kasa da kasa.

Ya kara da cewa, Sin na son yin aiki tare da Habasha wajen aiwatar da manufar zaman lafiya da ci gaba a yankin kahon Afirka, da tallafa wa jama’ar Afirka wajen warware matsalolin Afirka ta hanyar da ta dace da Afirka.

A nasa bangaren, Mekonnen ya bayyana cewa, kasar Habasha tana da dadadden tarihi wajen raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin, kuma tana da niyyar karfafa hadin gwiwar dake tsakaninta da kasar Sin a matakan kasashen biyu, da shiyya-shiyya da kuma sassa daban-daban.

Ya ce, Habasha ta yaba da irin taimakon da kasar Sin take ba ta, wajen kiyaye tsaro da zaman lafiyarta, tana kuma fatan kasar Sin za ta kara taimaka mata wajen tabbatar da zaman lafiya, da aiwatar da gyare-gyare, da ma farfado da tattalin arzikinta yadda ya kamata.

Bugu da kari, shugaban kasar Kenya William Samoei Ruto, ya gana da Mr. Wang Yi a birnin Nairobi na kasar Kenya a yau Asabar, inda bangaorin 2 suka bayyana niyyar raya huldar dake tsakanin kasashen 2 zuwa wani sabon mataki. (Ibrahim Yaya, Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasuwar Gero A Duniya Za Ta Kai Dala Biliyan 12 A 2025 -Masana

Next Post

Duk Shekara Ana Samun Dala Biliyan 450 A Fannin Kiwon Zuma -Masana

Related

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

1 hour ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

2 hours ago
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 
Daga Birnin Sin

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

3 hours ago
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

4 hours ago
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
Daga Birnin Sin

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

5 hours ago
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

23 hours ago
Next Post
Duk Shekara Ana Samun Dala Biliyan 450 A Fannin Kiwon Zuma -Masana

Duk Shekara Ana Samun Dala Biliyan 450 A Fannin Kiwon Zuma -Masana

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.