• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Kasashen Habasha Da Kenya Sun Gana Da Wang Yi

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugabannin Kasashen Habasha Da Kenya Sun Gana Da Wang Yi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Firaministan Habasha Abiy Ahmed, ya gana da daraktan ofishin kula da harkokin waje na kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin (JKS) Wang Yi jiya Jumma’a, inda bangarorin biyu suka yi alkawarin inganta hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.

Wang Yi ya kai ziyara kasar Habasha ne a kan hanyarsa ta hakartar taron masu ba da shawara kan harkokin tsaron kasa na kasashen BRICS karo na 13, da zai gudana a birnin Johannesburg na Afirka ta Kudu.

  • Masani Habasha Ya Yi Karin Haske Kan Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

A yayin ganawarsa da Wang, Abiy Ahmed ya yi karin haske kan manyan nasarorin da kasar Sin ta cimma, yayin da take bin tafarkin gurguzu mai sigar musamman na kasar Sin, yana mai cewa, ya yaba da yadda kasar Sin take nacewa kan tafarkin ci gaba da ya dace da yanayin kasarta, gami da saurin bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewa da ta samu, wanda ya zama abin koyi ga ragowar kasashe masu tasowa.

A nasa bangaren kuwa, Wang Yi ya bayyana cewa, Habasha babbar kasa ce a nahiyar Afirka da ke da tasiri mai mahimmanci. Yana mai cewa a matsayinsu na abokan huldar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare, Sin da Habasha suna da buri daya, kuma sun gudanar da hadin gwiwa mai inganci bisa tsare-tsare irin su “shawarar ziri daya da hanya daya” da dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka, wanda ke jagorantar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka.

Ban da haka, Wang Yi shi ma ya gana da mataimakin firaministan kasar Habasha kuma ministan harkokin wajen kasar Demeke Mekonnen.

Labarai Masu Nasaba

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Yayin ganawar, Wang ya ce, kasar Sin tana goyon bayan kasar Habasha wajen kiyaye ikonta mulkin da cikakkun yankunanta, da goyon bayan kasar wajen cika alkawarin da ta dauka na tabbatar da hadin kai da zaman lafiyar kasar, tana kuma goyon bayanta wajen taka muhimmiyar rawa a harkokin shiyya-shiyya da na kasa da kasa.

Ya kara da cewa, Sin na son yin aiki tare da Habasha wajen aiwatar da manufar zaman lafiya da ci gaba a yankin kahon Afirka, da tallafa wa jama’ar Afirka wajen warware matsalolin Afirka ta hanyar da ta dace da Afirka.

A nasa bangaren, Mekonnen ya bayyana cewa, kasar Habasha tana da dadadden tarihi wajen raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin, kuma tana da niyyar karfafa hadin gwiwar dake tsakaninta da kasar Sin a matakan kasashen biyu, da shiyya-shiyya da kuma sassa daban-daban.

Ya ce, Habasha ta yaba da irin taimakon da kasar Sin take ba ta, wajen kiyaye tsaro da zaman lafiyarta, tana kuma fatan kasar Sin za ta kara taimaka mata wajen tabbatar da zaman lafiya, da aiwatar da gyare-gyare, da ma farfado da tattalin arzikinta yadda ya kamata.

Bugu da kari, shugaban kasar Kenya William Samoei Ruto, ya gana da Mr. Wang Yi a birnin Nairobi na kasar Kenya a yau Asabar, inda bangaorin 2 suka bayyana niyyar raya huldar dake tsakanin kasashen 2 zuwa wani sabon mataki. (Ibrahim Yaya, Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasuwar Gero A Duniya Za Ta Kai Dala Biliyan 12 A 2025 -Masana

Next Post

Duk Shekara Ana Samun Dala Biliyan 450 A Fannin Kiwon Zuma -Masana

Related

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

54 minutes ago
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

22 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

23 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

24 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

1 day ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

1 day ago
Next Post
Duk Shekara Ana Samun Dala Biliyan 450 A Fannin Kiwon Zuma -Masana

Duk Shekara Ana Samun Dala Biliyan 450 A Fannin Kiwon Zuma -Masana

LABARAI MASU NASABA

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

October 5, 2025
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

October 5, 2025
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.