• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Sun Yi Alkawarin Kara Hadin Gwiwa Da Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Sun Yi Alkawarin Kara Hadin Gwiwa Da Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabanni daga kasashen tsakiyar Asiya, sun jaddada muhimmancin shawarar ziri daya da hanya daya, BRI a takaice, tare da bayyana goyon bayansu ga sanarwar Xi’an, yayin taron kolin kasashen Sin da tsakiyar Asiya da aka yi jiya Jumma’a a birnin Xi’an na lardin Shaanxi dake yankin arewa maso yammacin kasar Sin.

Shugabannin sun kuma yi tsokaci sosai kan ra’ayin shugaban kasar Sin Xi Jinping, na gina al’umma mai makomar bai daya ga daukacin bil-Adama, da shirin raya kasa da kasa, da samar da tsaro a duniya, da shirin wayewar kai a duniya.

  • Babban Mai Ba Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Na Kasar Sin Ya Gana Da Manyan Mambobin Kungiyar Musulmai Ta Kasar Sin

Za kuma su yi amfani da bikin cika shekaru 10 da kirkiro shawarar, a matsayin wata dama ta inganta hadin gwiwa a shiyyar, da zurfafa hadin gwiwa a fannoni daban-daban, da kara kusanto da al’ummar Sin da tsakiyar Asiya mai makomar bai daya.

Game da wannan taron kolin shugabannin kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya da aka shirya a birnin Xi’an, fadar mulkin lardin Shaanxi dake arewa maso yammacin kasar Sin tsakanin ranakun 18 zuwa 19, mamban majalisar gudanarwar kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Qin Gang ya zanta da manema labarai jiya, inda ya bayyana cewa, matsayar da aka cimma game da gina kyakkyawar makomar Sin da kasashen tsakiyar Asiya babban sakamakon siyasa ne da aka samu yayin taron.

Qin Gang ya yi tsokaci da cewa, taron kolin yana da ma’anar tarihi saboda, shi ne karo na farko da aka kira taron, tun bayan da aka kafa tsarin hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya shekaru uku da suka gabata.

Labarai Masu Nasaba

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

Kuma shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da muhimmin jawabi yayin taron, inda ya gabatar da matakai hudu kan yadda za a gina kyakkyawar makomar Sin da kasashen tsakiyar Asiya ta bai daya, kana ya gabatar da shawarwari guda takwas kan hadin gwiwar dake tsakanin sassan biyu, wannan shi ne karo na farko da shugaban kolin kasar Sin ya yi cikakken bayani kan manufofin huldarta da kasashen yankin tsakiyar Asiya a sabon zamanin da ake ciki, manufofin da suka samu yabo da amincewa matuka daga shugabannin kasashen yankin da suka halarci taron.

Hakazalika kasar Sin da kasashe biyar dake yankin tsakiyar Asiya, sun sa hannu kan takardu guda bakwai wadanda suka hada da “sanarwar Xi’an ta taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya”, da “sakamakon taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya” da sauransu, kana sun daddale yarjejeniyoyi sama da 100 dake shafar fannoni daban daban, ana iya cewa, tasirin taron kolin, yana da girma kuma ba a taba ganin irinsa a tarihi ba.

Ban da haka, Qin Gang ya jaddada cewa, kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya, ba za su mayar da wata kasa saniyar ware ba yayin da suke gudanar da hadin gwiwar dake tsakaninsu, kuma za su yi kokari tare da sauran kasashen duniya, domin ingiza ci gaban duniya baki daya.

Sannan a yau Asabar, kafar CMG ta sharhanta cewa, an yi nasarar shirya taron kolin shugabannin kasar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya guda biyar karo na farko, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da wani muhimmin jawabi yayin taron, inda ya jaddada cewa, duniyarmu tana bukatar yankin tsakiyar Asiya mai kwanciyar hankali da wadata da zaman jituwa dake cudanyar juna, kana ya gabatar da matakai hudu kan yadda za a gina kyakkyawar makomar Sin da kasashen tsakiyar Asiya ta bai daya, kana ya bayar da shawarwari guda takwas kan hadin gwiwar dake tsakanin sassan biyu, duk wadannan sun samu yabo da amincewa matuka daga shugabannin kasashen yankin mahalartan taron.

Taron ya kasance taron da kasar Sin ta kira a zahiri na farko, tun bayan da ta kulla huldar diplomasiyya da kasashen yankin tsakiyar Asiya, kana shi ne taron koli karo na farko da ta kira tun bayan da aka kafa tsarin hadin gwiwar dake tsakanin Sin da kasashen tsakiyar Asiya shekaru uku da suka gabata.

A halin yanzu duniyarmu tana fama da manyan sauye-sauye, don haka kasar Sin da kasashe biyar dake yankin tsakiyar Asiya, suna fuskantar jarrabawa mai sarkakiya, kuma dukkansu suna kokarin raya kasashensu, shi ya sa huldar dake tsakaninsu tana kara zurfafa yadda ya kamata.

Kamar yadda shugaba Xi ya fada wato gina kyakkyawar makomar Sin da kasashen tsakiyar Asiya ta bai daya, zabi ne mai ma’anar tarihi da suka yi bisa la’akari da babbar moriyar al’ummomin kasashen da makomarsu mai haske. (Mai fassarawa: Ibrahim Yaya, Jamila Zhou)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ta Bukaci Aiki Tare Da Sabuwar Gwamnatin Tinubu

Next Post

Yanzu-Yanzu: Tinubu Ya Dawo Nijeriya Gabanin Rantsar Da Shi

Related

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

17 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

19 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

20 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

21 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

2 days ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

2 days ago
Next Post
Yanzu-Yanzu: Tinubu Ya Dawo Nijeriya Gabanin Rantsar Da Shi

Yanzu-Yanzu: Tinubu Ya Dawo Nijeriya Gabanin Rantsar Da Shi

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.