• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Sun Yi Alkawarin Kara Hadin Gwiwa Da Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Sun Yi Alkawarin Kara Hadin Gwiwa Da Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabanni daga kasashen tsakiyar Asiya, sun jaddada muhimmancin shawarar ziri daya da hanya daya, BRI a takaice, tare da bayyana goyon bayansu ga sanarwar Xi’an, yayin taron kolin kasashen Sin da tsakiyar Asiya da aka yi jiya Jumma’a a birnin Xi’an na lardin Shaanxi dake yankin arewa maso yammacin kasar Sin.

Shugabannin sun kuma yi tsokaci sosai kan ra’ayin shugaban kasar Sin Xi Jinping, na gina al’umma mai makomar bai daya ga daukacin bil-Adama, da shirin raya kasa da kasa, da samar da tsaro a duniya, da shirin wayewar kai a duniya.

  • Babban Mai Ba Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Na Kasar Sin Ya Gana Da Manyan Mambobin Kungiyar Musulmai Ta Kasar Sin

Za kuma su yi amfani da bikin cika shekaru 10 da kirkiro shawarar, a matsayin wata dama ta inganta hadin gwiwa a shiyyar, da zurfafa hadin gwiwa a fannoni daban-daban, da kara kusanto da al’ummar Sin da tsakiyar Asiya mai makomar bai daya.

Game da wannan taron kolin shugabannin kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya da aka shirya a birnin Xi’an, fadar mulkin lardin Shaanxi dake arewa maso yammacin kasar Sin tsakanin ranakun 18 zuwa 19, mamban majalisar gudanarwar kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Qin Gang ya zanta da manema labarai jiya, inda ya bayyana cewa, matsayar da aka cimma game da gina kyakkyawar makomar Sin da kasashen tsakiyar Asiya babban sakamakon siyasa ne da aka samu yayin taron.

Qin Gang ya yi tsokaci da cewa, taron kolin yana da ma’anar tarihi saboda, shi ne karo na farko da aka kira taron, tun bayan da aka kafa tsarin hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya shekaru uku da suka gabata.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Kuma shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da muhimmin jawabi yayin taron, inda ya gabatar da matakai hudu kan yadda za a gina kyakkyawar makomar Sin da kasashen tsakiyar Asiya ta bai daya, kana ya gabatar da shawarwari guda takwas kan hadin gwiwar dake tsakanin sassan biyu, wannan shi ne karo na farko da shugaban kolin kasar Sin ya yi cikakken bayani kan manufofin huldarta da kasashen yankin tsakiyar Asiya a sabon zamanin da ake ciki, manufofin da suka samu yabo da amincewa matuka daga shugabannin kasashen yankin da suka halarci taron.

Hakazalika kasar Sin da kasashe biyar dake yankin tsakiyar Asiya, sun sa hannu kan takardu guda bakwai wadanda suka hada da “sanarwar Xi’an ta taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya”, da “sakamakon taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya” da sauransu, kana sun daddale yarjejeniyoyi sama da 100 dake shafar fannoni daban daban, ana iya cewa, tasirin taron kolin, yana da girma kuma ba a taba ganin irinsa a tarihi ba.

Ban da haka, Qin Gang ya jaddada cewa, kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya, ba za su mayar da wata kasa saniyar ware ba yayin da suke gudanar da hadin gwiwar dake tsakaninsu, kuma za su yi kokari tare da sauran kasashen duniya, domin ingiza ci gaban duniya baki daya.

Sannan a yau Asabar, kafar CMG ta sharhanta cewa, an yi nasarar shirya taron kolin shugabannin kasar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya guda biyar karo na farko, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da wani muhimmin jawabi yayin taron, inda ya jaddada cewa, duniyarmu tana bukatar yankin tsakiyar Asiya mai kwanciyar hankali da wadata da zaman jituwa dake cudanyar juna, kana ya gabatar da matakai hudu kan yadda za a gina kyakkyawar makomar Sin da kasashen tsakiyar Asiya ta bai daya, kana ya bayar da shawarwari guda takwas kan hadin gwiwar dake tsakanin sassan biyu, duk wadannan sun samu yabo da amincewa matuka daga shugabannin kasashen yankin mahalartan taron.

Taron ya kasance taron da kasar Sin ta kira a zahiri na farko, tun bayan da ta kulla huldar diplomasiyya da kasashen yankin tsakiyar Asiya, kana shi ne taron koli karo na farko da ta kira tun bayan da aka kafa tsarin hadin gwiwar dake tsakanin Sin da kasashen tsakiyar Asiya shekaru uku da suka gabata.

A halin yanzu duniyarmu tana fama da manyan sauye-sauye, don haka kasar Sin da kasashe biyar dake yankin tsakiyar Asiya, suna fuskantar jarrabawa mai sarkakiya, kuma dukkansu suna kokarin raya kasashensu, shi ya sa huldar dake tsakaninsu tana kara zurfafa yadda ya kamata.

Kamar yadda shugaba Xi ya fada wato gina kyakkyawar makomar Sin da kasashen tsakiyar Asiya ta bai daya, zabi ne mai ma’anar tarihi da suka yi bisa la’akari da babbar moriyar al’ummomin kasashen da makomarsu mai haske. (Mai fassarawa: Ibrahim Yaya, Jamila Zhou)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ta Bukaci Aiki Tare Da Sabuwar Gwamnatin Tinubu

Next Post

Yanzu-Yanzu: Tinubu Ya Dawo Nijeriya Gabanin Rantsar Da Shi

Related

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

8 hours ago
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

9 hours ago
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

10 hours ago
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar
Daga Birnin Sin

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

11 hours ago
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha
Daga Birnin Sin

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

12 hours ago
Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6
Daga Birnin Sin

Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

13 hours ago
Next Post
Yanzu-Yanzu: Tinubu Ya Dawo Nijeriya Gabanin Rantsar Da Shi

Yanzu-Yanzu: Tinubu Ya Dawo Nijeriya Gabanin Rantsar Da Shi

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.