ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Sun Yi Alkawarin Kara Hadin Gwiwa Da Sin

by CMG Hausa
3 years ago
Asiya

Shugabanni daga kasashen tsakiyar Asiya, sun jaddada muhimmancin shawarar ziri daya da hanya daya, BRI a takaice, tare da bayyana goyon bayansu ga sanarwar Xi’an, yayin taron kolin kasashen Sin da tsakiyar Asiya da aka yi jiya Jumma’a a birnin Xi’an na lardin Shaanxi dake yankin arewa maso yammacin kasar Sin.

Shugabannin sun kuma yi tsokaci sosai kan ra’ayin shugaban kasar Sin Xi Jinping, na gina al’umma mai makomar bai daya ga daukacin bil-Adama, da shirin raya kasa da kasa, da samar da tsaro a duniya, da shirin wayewar kai a duniya.

  • Babban Mai Ba Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Na Kasar Sin Ya Gana Da Manyan Mambobin Kungiyar Musulmai Ta Kasar Sin

Za kuma su yi amfani da bikin cika shekaru 10 da kirkiro shawarar, a matsayin wata dama ta inganta hadin gwiwa a shiyyar, da zurfafa hadin gwiwa a fannoni daban-daban, da kara kusanto da al’ummar Sin da tsakiyar Asiya mai makomar bai daya.

ADVERTISEMENT

Game da wannan taron kolin shugabannin kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya da aka shirya a birnin Xi’an, fadar mulkin lardin Shaanxi dake arewa maso yammacin kasar Sin tsakanin ranakun 18 zuwa 19, mamban majalisar gudanarwar kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Qin Gang ya zanta da manema labarai jiya, inda ya bayyana cewa, matsayar da aka cimma game da gina kyakkyawar makomar Sin da kasashen tsakiyar Asiya babban sakamakon siyasa ne da aka samu yayin taron.

Qin Gang ya yi tsokaci da cewa, taron kolin yana da ma’anar tarihi saboda, shi ne karo na farko da aka kira taron, tun bayan da aka kafa tsarin hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya shekaru uku da suka gabata.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Kuma shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da muhimmin jawabi yayin taron, inda ya gabatar da matakai hudu kan yadda za a gina kyakkyawar makomar Sin da kasashen tsakiyar Asiya ta bai daya, kana ya gabatar da shawarwari guda takwas kan hadin gwiwar dake tsakanin sassan biyu, wannan shi ne karo na farko da shugaban kolin kasar Sin ya yi cikakken bayani kan manufofin huldarta da kasashen yankin tsakiyar Asiya a sabon zamanin da ake ciki, manufofin da suka samu yabo da amincewa matuka daga shugabannin kasashen yankin da suka halarci taron.

Hakazalika kasar Sin da kasashe biyar dake yankin tsakiyar Asiya, sun sa hannu kan takardu guda bakwai wadanda suka hada da “sanarwar Xi’an ta taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya”, da “sakamakon taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya” da sauransu, kana sun daddale yarjejeniyoyi sama da 100 dake shafar fannoni daban daban, ana iya cewa, tasirin taron kolin, yana da girma kuma ba a taba ganin irinsa a tarihi ba.

Ban da haka, Qin Gang ya jaddada cewa, kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya, ba za su mayar da wata kasa saniyar ware ba yayin da suke gudanar da hadin gwiwar dake tsakaninsu, kuma za su yi kokari tare da sauran kasashen duniya, domin ingiza ci gaban duniya baki daya.

Sannan a yau Asabar, kafar CMG ta sharhanta cewa, an yi nasarar shirya taron kolin shugabannin kasar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya guda biyar karo na farko, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da wani muhimmin jawabi yayin taron, inda ya jaddada cewa, duniyarmu tana bukatar yankin tsakiyar Asiya mai kwanciyar hankali da wadata da zaman jituwa dake cudanyar juna, kana ya gabatar da matakai hudu kan yadda za a gina kyakkyawar makomar Sin da kasashen tsakiyar Asiya ta bai daya, kana ya bayar da shawarwari guda takwas kan hadin gwiwar dake tsakanin sassan biyu, duk wadannan sun samu yabo da amincewa matuka daga shugabannin kasashen yankin mahalartan taron.

Taron ya kasance taron da kasar Sin ta kira a zahiri na farko, tun bayan da ta kulla huldar diplomasiyya da kasashen yankin tsakiyar Asiya, kana shi ne taron koli karo na farko da ta kira tun bayan da aka kafa tsarin hadin gwiwar dake tsakanin Sin da kasashen tsakiyar Asiya shekaru uku da suka gabata.

A halin yanzu duniyarmu tana fama da manyan sauye-sauye, don haka kasar Sin da kasashe biyar dake yankin tsakiyar Asiya, suna fuskantar jarrabawa mai sarkakiya, kuma dukkansu suna kokarin raya kasashensu, shi ya sa huldar dake tsakaninsu tana kara zurfafa yadda ya kamata.

Kamar yadda shugaba Xi ya fada wato gina kyakkyawar makomar Sin da kasashen tsakiyar Asiya ta bai daya, zabi ne mai ma’anar tarihi da suka yi bisa la’akari da babbar moriyar al’ummomin kasashen da makomarsu mai haske. (Mai fassarawa: Ibrahim Yaya, Jamila Zhou)

Asiya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Next Post
Yanzu-Yanzu: Tinubu Ya Dawo Nijeriya Gabanin Rantsar Da Shi

Yanzu-Yanzu: Tinubu Ya Dawo Nijeriya Gabanin Rantsar Da Shi

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.