• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Kungiyoyi Da Kafofin Watsa Labarai Na Kasa Da Kasa Suna Fatan Za Su Kara Zurafa Hadin Gwiwa Da CMG

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
cmg
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A gabannin sabuwar shekara ta 2023, wasu shugabannin kungiyoyin kasa da kasa kamar su hukumar kula da wasannin Olympics ta kasa da kasa, da asusun gina karfin nahiyar Afirka wato ACBF, da wasu shugabannin kafofin watsa labarai na kasa da kasa da suka hada da hukumar kula da kafofin watsa labarai na kasar Kenya, da gidan rediyon kasar Gabon sun aike da sakon murnar zuwan sabuwar shekara ga shugaba kuma babban edita na babban gidan rediyo da talibijin na kasar Sin wato CMG Shen Haixiong, inda suka nuna fatansu na ci gaba da kara zurfafa cudanya da hadin gwiwa dake tsakaninsu da CMG.

A cikin sakonsa, shugaban hukumar kula da wasannin Olympics ta kasa da kasa Thomas Bach ya nuna babbar godiyarsa ga shugaban CMG Shen Haixiong saboda goyon bayan da yake nunawa wasannin Olympics, da alkawarin da ya cika kan wasannin.

Shugaban zartaswa na asusun gina karfin nahiyar Afirka kuma tsohon mataimakin shugaban hukumar AU Erastus Mwencha ya bayyana cikin sakonsa cewa, yana fatan za a gudanar da hadin gwiwa dake tsakanin asusunsa da CMG yadda ya kamata a sabuwar shekara dake tafe.

Babban jami’in zartaswa na hukumar kula da kafofn watsa labarai na Kenya David Omwoyo ya yi tsokaci cewa, yana fatan za a bude wani sabon shafi na hadin gwiwar dake tsakanin kafofin watsa labarai na kasarsa da CMG.

Haka zalika shugaban gidan talibijin na kasar Gabon Ali Reynald Radjoumba ya bayyana cewa, yana sa ran gidan talibijin din da CMG za su kara zurfafa hadin gwiwa a shekarar 2023 domin samun ci gaba tare.

Labarai Masu Nasaba

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

A nasa bangare, shugaban CMG Shen Haixiong shi ma ya yi musu fatan alheri a sabuwar shekara, kuma ya bayyana cewa, babban taron wakilan JKS da ya kammala cikin nasara ba da dadewa ba, ya kara kuzuri ga hadin gwiwar sada zumunta tsakanin kasar Sin da sauran kasashen duniya.

Ya kara da cewa, CMG yana son ci gaba da taka rawarsa ta kasancewa gada domin ba da gudummowarsa kan wanzar da zaman lafiya da samar da wadata ga al’ummar kasashen duniya tare da kungiyoyi da kafofin watsa labarai na kasa da kasa. (Mai fassarawa: Jamila daga CMG Hausa)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zan Fi Mayar Da Hankali Kan Ilimi Da Matasa – Kwankwaso

Next Post

Xi Da Takwaransa Na Benin Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Sake Daddale Huldar Diplomasiya

Related

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

12 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

13 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

14 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

15 hours ago
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

16 hours ago
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154
Daga Birnin Sin

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

17 hours ago
Next Post
Xi Da Takwaransa Na Benin Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Sake Daddale Huldar Diplomasiya

Xi Da Takwaransa Na Benin Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Sake Daddale Huldar Diplomasiya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.