• English
  • Business News
Wednesday, July 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabar Matan NNPP Ta Nemi Mata Su Yi Rajistar Katin Zabe

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
NNPP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon da ya gaba ne, Shugabar Matan Jam’iyyar NNPP reshen Babban Birnin Tarayya Abuja, Hajiya Saudat Abdullahi, ta karbi bakuncin shugaban jam’iyyar na kasa a sakariyar jam’iyyar ta Abuja, yayin da ya kai ziyara sakatariyar domin jinjina musu kan namijin kokarin da suke yi na ganin jam’iyyar ta sake samun karbuwa.

A jawabin da ya gabatar, shugaban jam’iyyar na kasa Farfesa Ahmed Rufa’i Alkali, ya ce sun zo domin ziyara ta musamman ga ‘yan jam’iyyar da kuma kara musu kwarin gwiwar ci gaba da kokarin da suke yi na ganin an kai ga cimma nasarar abin da suka sa a gaba.
“Mun zo ne mu ga wannan ofis ne na mutanenmu dake FCT wanda kuma ka san cibiyar kasa ce.

  • Rahoton Karya Da Adrian Zenz Ya Watsa Ya Tona Asirin Amurka

Mutane ne masu kishin wannan jam’iyya kuma sun yi abubuwa da dama na kasaita, shi ne muka ya dace mu zo, don haka shugabannin wannan jam’iyya na kasa gaba daya muka hallara a nan domin mu jinjina musu, kuma mu gaisa da su.

Sannan muna rokonsu da su ci gaba da aiki mai kyau, musammam magana neman mambobi, kada a karaya, a ci gaba da neman jama’a in kuma an same su to a ci gaba jan hankalinsu da su yi rajista, rajistar jam’iyya da kuma rajistar INEC wato wacce za su yi zabe da ita,” in ji shi.

A cewarsa, dalilin da ya sa ya sa a yi rajistar zabe, idana aka zo zabe katin zaben nan shi aka sani, in baka da shi to ba za ka amfani kowa ba, to gaskiya mun gode da irin yadda shi Alhaji Dauda shugaban jam’iyya na FCT da kuma Hajiya Saudat shugabar mata suke nunawa da sauran jama’arsu, Allah ya saka musu da alheri.

Labarai Masu Nasaba

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

A zantawarta da wakilimmu bayan kammala ziyarar, Shugabar Matan Jam’iyyar ta NNPP ta Babban Birnin Tarayya Abuja, Hajiya Saudat Abdullahi, kira ta yi ga jama’a musamman mata dake fadin tarayyar kasar nan da su tabbataba sun karbi katin zabe, domin a cewarta akwai jam’iyyu kamar APC da PDP, wadanda tuni sun taka rawarsu ta fuskar gudanar da shugabancin kasar nan kowa ya gani ya kuma shaida abin da suka yi, kuma mun ga yadda suka mayar da kasar, an mayar da mutane kamar ba mutane ba, kasa babu tsaro, tattalin arzikin ya karye, ga tsadar abubuwan yau da kullum, ga bashi ya yi wa kasar katutu.

A don haka ta ga dacewar kira gare su da kada su yi kasa a gwiwa wajen ganin sun riki katin zabensu domin sai da katin zabe ne mutum zai iya sauya gwamnatin da yake son canjawa.

Da aka tambaye ta ko yaya take ganin karbuwar jam’iyyar a babban birnin tarayya, duba da cewa akwai manyan jam’iyyu a gabansu? Sai ta ce, eh lallai haka ne, akwai jam’iyyu manya kamar PDP da APC wacce a yanzu ke mulki, to ai kasancewarsu manyan jam’iyyu ba shi yake nuna kullum su za su ci gaba mulki a kasar nan ba, domin kuwa an yi wata jam’iyya da yi mulki a baya kamar NPN karkashin shugabancin Marigayi Shehu Shagari, to yanzu ina NPN take, ka ga ta wuce, don haka duk abin da ya yi zamaninsa yana iya kaucewa ya bar wa wani shi ma ya yi nasa zamanin, saboda haka yanzu NNPP ta yunkuro kuma babu gudu babu ja baya, za ta ba wa mamaki domin shi mulki na Allah kuma a wurin Allah muke nema, in sha Allah za mu yi nasara.

“Wannan jam’iyya ta shigo ne da nufin in har Allah ya sa muka kafa gwamnati za mu mayar da Nijeriya ta zama sabuwa, ta hanyar samar da ingantaccen tsaro, mutum zai yi tafiya kamar yadda ake yi a baya ba tare da jin wata fargaba ba, sannan kuma ilimi da shi ma a yanzu yake cikin halin ha’ula’i dole a yi gyara, da kuma samar da hanyoyin da za’a tallafa wa mata matasa da yara domin su tsaya da kafarsu, kuma hakan za a yi ne ba tare da nuna banbancin kabila addini ko bangaranci ba“, in ji ta.

Ta yi kira ga mata da su rungumi jamíyyar NNPP domin ita ce jam’iyyar da take burin fitar da talakawa daga mawuyacin halin da suka tsinci kansu a ciki na talauci da fatara.

“Ina kira ga mata da su fito kwansu da kwarkwatarsu, domin wannan jam’iyyar tasu ce, kuma har yanzu a rajista ba a rufe ba, su adana saboda ranar zabe su fito domin kada kuri’arsu.

Mun karbi mata da yawa da suke da wannan rajista, wadanda ba su da ita muna umartar su da su je yanki ta su rajistar, domin an sake kara lokaci, don haka ina kira ga mata da su yi tsayin daka wajen ganin sun yi wannan babban zabe tanadi, ya zama muna tare da su ko ina madugu zai tafi muna tare kafarsa kafarmu”, in ji ta.

Ta ci gaba da cewa a wannan tafiya ta mudugu idan har Allah ya sa mun kai ga samun nasara, to kowa za a yi masa abin ya dace domin Nijeriya aka ce, duk dan Nijriya kuma ya cancanci a kyautata masa, sawa’un daga Kudu yake ko Arewa babu banbanci in dai dan Nijeriya ne, kuma duk ayyukan da aka yi a kowace jiha shi za a yi a sauran jihohin. Sannan ta yi kira ga dukkan mambobin jam’iyyar da su ci gaba da jajircewa wajen nuna kishi da son jam’iyyar, sannan su guji nuna banbanci na kabilanci ko bangaranci, kazalika ta yi kira ga matasa da guji shiga siyasar daba, da ta’ammali da miyagun kwayoyi, a cewarta yin ta’ammali da miyagun kwayoyi shi kan sanya su afkawa cikin haramtattun kungiyoyi.

A karshe ta yi addu’ar Allah ya zaunar Nijeriya lafiya, ya kawo yalwal arziki, ya ba wa jama’iyyar NNPP nasara a dukkan al’amuran da ta sa a gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Nuna Adawa Da Kudurin Majalisar Turai Kan Xinjiang

Next Post

Cinikayyar Wajen Sin Ya Farfado Sakamakon Daukar Kwararan Matakan Farfadowar Tattalin Arziki

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

4 days ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

4 days ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

1 week ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

2 weeks ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

2 weeks ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

2 weeks ago
Next Post
Cinikayyar Wajen Sin Ya Farfado Sakamakon Daukar Kwararan Matakan Farfadowar Tattalin Arziki

Cinikayyar Wajen Sin Ya Farfado Sakamakon Daukar Kwararan Matakan Farfadowar Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

July 22, 2025
Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

July 22, 2025
Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

July 22, 2025
Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

July 22, 2025
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

July 22, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

July 22, 2025
Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

July 22, 2025
Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

July 22, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

July 22, 2025
Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

July 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.