• Leadership Hausa
Sunday, August 14, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Daga Birnin Sin

Rahoton Karya Da Adrian Zenz Ya Watsa Ya Tona Asirin Amurka

by CMG Hausa
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Rahoton Karya Da Adrian Zenz Ya Watsa Ya Tona Asirin Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata doka mai suna wai hana tilastawa ‘yan Uygur aiki ta Amurka za ta fara aiki nan bada jimawa ba.

Kwanan nan, Adrian Zenz, wanda ya sha kitsa karairayi ya sake fitar da wani rahoton dake nuna cewa, wai kasar Sin na kara tilastawa mutane aiki. Irin wannan doka tana cike da karairayi, wadda ta tona asirin kasar Amurka, na kawar da Xinjiang daga cikin yankuna masu samar da kayayyaki ga duniya.

Hakika, kafofin watsa labarai sun ruwaito maganganun tsoffin ‘yan diflomasiyyar Amurka a kasar Sin dake cewa, babu wata matsala a Xinjiang, dukkanmu mun sani, amma yin amfani da jihar Xinjiang don rura wutar rikici kan batutuwan da suka shafi tilasta yin aiki, da kisan kare-dangi, da kuma keta hakkin dan Adam, dabara ce ta tsunduma gwamnatin kasar Sin cikin mummunan mawuyacin hali.

Rahoton karya da Adrian Zenz ya fitar a wannan karo, yana cewa, wai duk da cewa shaidun da za’a iya amfani ba su da yawa, amma sabon ci gaban da ake samu, ya sa ake kara tilastawa mutane aiki, har zuwa wasu sana’o’in fasahohin zamani. Amma rahoton bai fayyace wane sabon ci gaba ba ne, kana bai bayyana shaidu da wasu alkaluma ba, illa karya ce zalla kawai.

A karshen bara, gwamnatin Amurka ta sa hannu kan wani shirin doka mai suna wai “hana tilastawa ‘yan Uygur aiki”, wanda za’a fara amfani da ita tun daga ranar 21 ga watan Yunin bana. Dokar za ta hana Amurka shigo da hajojin Xinjiang. Wato ta hanyar fakewa da batun hakkin dan Adam, wannan doka za ta hana ci gaban Xinjiang, da kwace damar samun bunkasuwa na mazauna yankin, kuma wannan take keta hakkin dan Adam ne a Xinjiang.

Labarai Masu Nasaba

Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar

Sin Ta Sanyawa Mataimakiyar Ministan Sufurin Kasar Lithuania Takunkumi

Kusan makwanni biyu da suka wuce, sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya yi jawabi kan manufofin gwamnatin Amurka game da kasar Sin, inda ya ambaci wasu muhimman kalmomi uku da suka hada da, zuba jari, kulla kawance, da yin takara.

Bisa fahimtar Amurka, yin takara shi ne matsa lamba ga abokan takara ta hanyar shafa musu bakin fenti, da kuma keta ka’idojin kasuwancin kasa da kasa, to, abin da mutum ya shuka, shi zai girba. (Murtala Zhang)

 

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwan Da Aka Halatta Da Wadanda Aka Haramta Ga Mahajjaci (II)

Next Post

Sin Ta Sake Neman Amurka Da Ta Bayyana Yadda Take Girmama Yarjejeniyar Haramta Makamai Masu Guba

Related

Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar

9 hours ago
Sin Ta Sanyawa Mataimakiyar Ministan Sufurin Kasar Lithuania Takunkumi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sanyawa Mataimakiyar Ministan Sufurin Kasar Lithuania Takunkumi

11 hours ago
An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing

12 hours ago
Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO

13 hours ago
Kungiyar Kawance Ta Sin Da Niger Na Goyon Bayan Manufar Sin Daya Tak
Daga Birnin Sin

Kungiyar Kawance Ta Sin Da Niger Na Goyon Bayan Manufar Sin Daya Tak

1 day ago
Wang Wenbin: Duk Irin Sauyin Yanayi Sin Za Ta Wanzar Da Fadada Bude Kofa
Daga Birnin Sin

Wang Wenbin: Duk Irin Sauyin Yanayi Sin Za Ta Wanzar Da Fadada Bude Kofa

1 day ago
Next Post
Sin Ta Sake Neman Amurka Da Ta Bayyana Yadda Take Girmama Yarjejeniyar Haramta Makamai Masu Guba

Sin Ta Sake Neman Amurka Da Ta Bayyana Yadda Take Girmama Yarjejeniyar Haramta Makamai Masu Guba

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Al’umma Su Ci Gaba Da Gudanar Da Addu’o’in Neman Zaman Lafiya

An Bukaci Al’umma Su Ci Gaba Da Gudanar Da Addu’o’in Neman Zaman Lafiya

August 13, 2022
EFCC Ta Cafke Malaman Addini 2 Da Wasu 5 Kan Zargin Damfara A Yanar Gizo A Kwara

EFCC Ta Cafke Malaman Addini 2 Da Wasu 5 Kan Zargin Damfara A Yanar Gizo A Kwara

August 13, 2022
Fiye Da Miliyan 326 Muka Biya Ma’aikata Da Suka Yi Ritaya A Shekarar Bara -Hukumar Fansho

Fiye Da Miliyan 326 Muka Biya Ma’aikata Da Suka Yi Ritaya A Shekarar Bara -Hukumar Fansho

August 13, 2022
Ganduje Ya Nada Shugabannin Gudanarwa Da Mambobin Hukumar Shari’a

Ganduje Ya Nada Shugabannin Gudanarwa Da Mambobin Hukumar Shari’a

August 13, 2022
Akwai Babban Aiki A Gaban Erik ten Hag A Man U

Akwai Babban Aiki A Gaban Erik ten Hag A Man U

August 13, 2022
Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar

Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar

August 13, 2022
Damfarar Miliyan 66: Kotu Ta Daure Maman Boko Haram Da Wasu Mutum 2

Damfarar Miliyan 66: Kotu Ta Daure Maman Boko Haram Da Wasu Mutum 2

August 13, 2022
Wacce Kungiya Za Ta Lashe Firimiyar Ingila?

Wacce Kungiya Za Ta Lashe Firimiyar Ingila?

August 13, 2022
Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Gudunmawar Naira Biliyan 2.5 Don Kammala Aikin Tashar Tsandauri

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Gudunmawar Naira Biliyan 2.5 Don Kammala Aikin Tashar Tsandauri

August 13, 2022
Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye Ne, Saurayi Ko Budurwa?

Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye Ne, Saurayi Ko Budurwa?

August 13, 2022
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.